Thursday, 28 June 2007

SARAKUNA DA MALAMAN ADDINI SUNA TARE DA TALAKAWA KUWA?

A jerin shugabannin al’umma a kasar mu Nijeriya ,Sarakuna da Malaman Addini nada matsayi da martaba na musamman kasantuwar su iyayen al’umma.Sun kasance fitilu masu haskakawa al’umma hanya kan yadda zasu tafi da rayuwar su bisa tsari da tarbiya kan tafarkin da sukayi imani dashi.Kuma sun kasance masu umarni ga al’umma kan aikata kyawawan aiyuka da gujewa munanan aiyuka.

Talakawa na matukar girmama su da amsar umarnin su saboda imanin da suke dashi na cewa baza su so duk wani abin da zai cutar da su ba.Amma sabanin irin rawar da sarakuna da malaman addini suka saba takawa, a yau mun wayi gari wasu daga cikin su sun sake salon tafiyar su ta wajen kasancewa tare da masu mulki da masu hannu da shuni.A yau a bayyane yake wasun su sun raba gari da talaka ,sun shiga tawagar masu mulki da masu hannu da shunin da suka dora kasar nan bisa tafarkin jari hujja da tsarin su talaka shine makiyi abin ki,saboda tsare tsaren su da manufofin su a kullum sai kara jefa talaka cikin halin kakani kani da bakar wahala suke kara tsunduma talaka.

Malaman addini a ko’ina cikin duniya an shaide su da a kullum da kasance tare da gaskiya kuma kira ga mabiyan su kan kamanta gaskiya da rikon amana .Basa tsoron fadin gaskiya komai dacinta .Sannan kuma basa hada kai da azzalumai da yan handama da masu halin fataken dare.Littatafan tarihin addini a cike yake da gwarazan malaman da sukayi kira da a daina zalunci,har ma wasun sun jagoranci al’umma ga kawar da zalunci da kama karya.A zamanin nan da muke ciki a idanun mu mun gan ko jin labaran malaman addinin da suka murkushe zalunci da azzalumai,dama malaman da aka daure su,ko aka tilasta masu gudun hijira ,koma aka raba su da rayukan su ba dan komai ba sai dan suna hani ga zalunci da danniya da wasu kalilan mutane suke yiwa mafi rinjayen mutane dan kawai tsarin tursasa al’umma na hannun su.

An wayi gari wasu malaman addini suna fassara littafan addinan su bisa tafarkin da zasu da’da’da wa masu mulki rai dan su sami abin duniya.Mun wayi gari in kayi fashin mulki ko magudin zabe zasu ce Allah ne ya baka! In ka saci dukiyar al’umma zasu ce Allah ne ya azurta ka!! In ka tursasa al’umma da karfin tsiya kan abinda sukayi intifakin basa so zasu ce Allah yace a bika!!! Kuma a yau mun wayi gari wasu malaman addini sune a kullum kan hanyar gidajen gwamnatocin jiha da tarrayya da gidajen wadanda kowa yasan ta hanyar da suka tara dukiyar su.

Ba wai ina cewa laifi bane ga sarakuna da malaman addini suyi mu’amala da masu mulki da masu hannu da shuni bane a’a matsalar shine na basa iya fada masu hakikanin gaskiyar halin da talakawa da kasa ke ciki.Talakawa na shan bakar wahalan da basu taba sha ba tun kafuwar kasar nan Nijeriya.Babu aikin yi da rashin magunguna a asibitoci da rashin wutar lantarki da rashin da babun suna da yawa.Amma wasu sarakuna da malaman addini sun tsuke bakunan su ,sun wayan ce kamar komai na tafiya dai dai! Kullum suka buda bakunan su sai kan talaka,sarakuna su fadawa talakawa su zauna lafiya ba tare da fadawa masu mulki suyi adalci ba, malaman addini kuma wa’azin su a kan talaka sukeyi kan ya daina kaza babu kyau ba tare da fadawa masu mulki su daina jefa talaka cikin matsi ba.
Babu ja kan cewa sarakuna da malaman addini suna da matsayi da martaba na musamman a al’ummar kasar nan.Shin matsayin da martaban bai ishe su bane suke tarewa a gindin masu mulki?Sannan akwai wani abin duniya da suka rasa shi yasa suka zama maroka ga masu mulki?Suna tsammanin kan mutane bai waye bane har yanzu suke fadin son zuciyar su a matsayin umarnin addini?Suna zaton cewa bin son zuciyan masu mulki shi zai kare masu kujerun su?Kuma sai a yaushe zasu samar wa kansu yanci a daina kiran su yan amshin shatan gwamnati?

A shugabannin al’umma a yanzu sarakuna da malaman addini ne kawai suka rage da talakawa kewa kallon da kyakyawan zato saboda imanin da suke dashi na cewa zasu yi masu jagoranci na gari da kare masu hakkokin su da samar masu kyakyawan yanayin da rayuwar su zata kasance cikin sauki da walwala.Shin ba babbar cin amana bane a ce a yau a matsayin su na jagorori sufi damuwa da samun biyan bukatun kan su kan na mabiyan su?Basa tunanin cewa talakawa na kallon su ,suna kuma iya yi masu irin nasu fassaran ,kuma masu iya magana na cewa mutumci madara ne in ya zube baya kwasuwa duka.

Tarihin kasashen turai da wasu a Asiya ya nuna irin rawar da sarakuna da malaman addini suka taka a baya. Me ya kawo karshen tasirun su a yau?amsa a bayyane yake ,saboda dasu aka hada kai da baki ana zaluntar talaka ,sun hada baki da masu mulki da kuma guguwar juyin juya hali yazo sai yayi awon gaba dasu gabaki daya.Shi yasa a wasu kasashen ma gabaki daya babu burbushin tsarin mulkin sarautar gargajiya,su kuma malaman addini suka rasa tasiri a rayuwar al’umma kan umartan su da kyakyawan aiki da hani ga mumunan aiki.

Ina sarakunan da suka tsayawa ,tare da daurewa masu magudin zabe gindi kan su zauna daram a kujerun su na mulki a kasar nan suke?Abinda yaci doma ba zai bar awai ba!Kuma tarihin kasar nan tun jamhuriya ta farko zuwa yau,sarakunan da suka bada hadin kai wajen dorawa talaka wanda bashi ya zaba ba na karewa da murabus!Haka ma duk malamin addinin daya hada baki da masu mulki na rasa girma da kima a idon jama’a dan suna ganin sa a matsayin malamin gwamnati.

Martaban sarakuna da malaman addini na iya karuwa sosai in suka martaba bukatun talaka da kare hakkokin sa.Su sami manufar fadawa masu mulki gaskiya koda a gaban sune,tare da basu shawarwarin da rayuwan talaka zata inganta da kuma kiran su dasu daina cigaba da duk manufofin dake kara jefa talaka cikin matsi.In kuma suka ziyarci gidajen gwamnati daga kananan hukumomi zuwa na tarayya ya kasance bukatun al’umma ne ya kaisu bawai samar wa kamfanonin su da ya’yan su kwangiloli da mukaman gwamnati ba .Yanda suke iya fadawa talaka gaskiya ,su iya fadawa masu mulki gaskiya.Kuma ya kamata a koda yaushe su kasance cikin sahun farko na kira ga gwamnati su canza duk wata manufa da al’umma ke kukan zai matsa masu,ba wai wasu daban su kasance a sahun gaba ba wajen kwatowa talaka yanci.

Shugabani na gari abin koyi ne ga talakawan su .Duk shugaban da ya sace dukiyar al’umma ko a baya ko a yanzu ya zama wajibi ga sarakuna da malaman addini su san irin mu’amalar da zasu yi dasu ,saboda rungumar su a jiki ke bada kwarin gwiwa ga yan’baya kan cewa suma za’a rungume su idan suka bada kudi aka gina wuraren ibadu da kuma kai gaisuwa fada ayi masu sarauta.Talakawa na tare da sarakuna da malaman addini ,da fatan suma kamar yanda ake martaba su,zasu cigaba da kasantuwa da talakawa,domin sabanin haka na iya janyowa talakawa su daina ganin kimar su wanda ka iya zama barazana ga al’umma gabaki daya domin in babba ya tsawatar aka ki sauraran sa to wa ke iya wannan babban aiki na dora al’umma bisa tafarkin shiriya?


Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Saturday, 2 June 2007

SAMAR DA SABUWAR TASWIYAR HANYA GA MATAN HAUSAWA

Mata a kasar Hausa sun kasance cikin matan da akafi kulawa da su da kokarin ganin sun sami nagartattacen rayuwa kan sauran mata na wasu bangarorin Nijeriya.Hukumomi ma basu yi kasa a gwiwa ba wajen taimakawa mata a inda a jihohi da dama ana basu ilimi kyauta da kulawa ta musamman in suna da juna biyu a asibitoci har zuwa haihuwa. A wannan makalar in mukayi zancen matan Hausawa sun kunshi dukkan matan dake zaune a Arewacin Nijeriya.Kan batun ma wanene Bahaushe ? Zamu barshi dan tattaunawa a wani lokacin .
Duk da a bayyane za'a ga kamar rayuwar matan Hausawa na tafiya ba tare da wata matsala ba, amma a hakikanin gaskiya akwai matsaloli da dama da al'umma suka tsuke bakunan su akai , kuma ba'a wani kokari na ganin an samar da mafita ga wadannan matsalolin .Bisa fahimtar addini da al'ada , da ci da sha da muhalli da tufafarwa duk sun ta'allaka akan miji ,amma kuma sai mazaje da mataye suka yiwa wannan umarnin addini da kuma al'ada wata fahimta ta daban .Wato ta bangaren maza suka noke da fahimtar samun wata dama da zasu dankwafar da mata ta hanyar kin basu damar da zasu inganta rayuwar su su kuma bada nasu gudunmawar ga cigaban ungwanin su da garin su da kasa gabaki daya .Su kuma mata sai suka fake da samun wannan damar na samun bukatun rayuwa bisa tsarin addini da al'ada ,sai yasa suka zauna suka mike kafa basa wani kokari ko yunkurin ganin rayuwar su ta inganta.
Kafin wasu su yi mani kartattacen fahimta , ina magana ne akan yadda rayuwar mata a kasar Hausa ta ta'allaka kan maza ba tare da yin wani yunkurin da rayuwar matan zata inganta su tsaya da kafafun su ba. Duk da cewa matsalolin tattalin arziki a yau ya tilasta wasu mazajen da mata su samar wa kan su mafita ta hanyar koyon sana'oi da kasuwanci da karatu mai zurfi ta fannin addini da boko dan samun ayyukan yi.Amma har yanzu akwai mazan da burin su shine yiwa matan su na aure mulkin mallaka ta wajen toshe duk wata hanyar da zasu sami kudin shiga.Wasu mazan kuma koda sunyi wa budurwa ko matan da zasu aura alkawarin cigaba da makaranta ko aiki,da zaran sun aure su sai suyi mirsisi su ki cika alkawarin da suka dauka.
Saboda hana mata samun kudin shiga ta hanyar aikin yi ko kasuwanci ko sana'a shike zafafa kishi yayin da mazajen su zasu kara aure domin suna ganin duk abinda mijin nasu ya mallaka wata cima zaune zata zo a raba da ita.Haka kuma so dayawa in mijin talaka ne wanda bai mallaki abin duniya ba ,da zarar ya mutu ko wata lalurar rashin lafiya ya sami mijin sai iyalen su shiga halin kakani kani. Ta kan kai da an bar matan da ya'ya, ya rage gare ta tasan yadda zata yi dasu.
Wai ma shin mun taba tambayar kawunan mu me yasa matan Hausawa ke daukan maganan gado da muhimmanci?Sannan kuma me kesa mai mata fiye da guda matan nasa zasu yi ta gasar haihuwa?Shin me ke kawo takun saka tsakanin matan marigayi da yan'uwan sa wajen rabon gado? Kuma me ke yawan kawo rabon gado a kotuna tsabanin shekarun baya da ake rabawa a gida?
Tun ranar gini tun ranar zane ,mafi yawan maza in suka je neman aure zancen da suka fi yiwa mata shine na basu aljannar duniya wanda ke jawo wasu yan'matan ma in makaranta ko aiki suke sai su daina domin kakar su ta yanke saka.Zai fi kyau tun ana neman auren a rika karfafa wa mata gwiwa domin su fuskanci rayuwa ,su kasance suna da manufa da burin da suke so su cimma a rayuwa.So dayawa irin wannan baiwar kan bayyana ga wasu matan yayin da mutuwa ta raba su da mazajen su ko rabuwan auren.Da dama sun shahara ta fannoni da dama da suka zabar wa kan su.
Matan Hausawa na bukatar sabon tsarin rayuwa da zasu taimakawa kan su da mazajen su da ya'yan su da iyayen su da yan'uwan su.Suna bukatar tallafi da karfafa gwiwa kan abinda suka zabar wa kan su a rayuwa.In sana'a take sha'awa ,to a tallafa mata wajen koyon sana'ar da kuma girmama su in akazo harkar cinikayya . Sannan in makaranta take sha'awa to a tallafa mata da taimaka mata har ta cimma wannan burin nata . Haka kuma in aiki zata yi a taimake ta dayi mata kyayawan zato.Ta wannan hanyar lallai mata zasu bada babban gudunmawa ga bunkasar tattalin arzikin kasa.
A zamanin nan da muke ciki da mafi yawan yaran da ake haihuwa mata ne ,akwai bukatar dora su bisa tafarkin da zasu zama masu dogaro da kan su saboda in suka sami kan su a halin mutuwan iyayen su ko mazan su na aure ,ko in auren su ya mutu ko kuma rashin samun mijin aure da wuri , ba zasu kasance cikin wani mumunan hali ba,su kasance suna masu iya dogaro da kan su dama taimakawa wasu.Kuma a wannan zamanin na jari hujja da gwamnati ta janye kusan dukkan tallafi kan abubuwan more rayuwa,magidanta da dama na shan bakar wahala wajen baiwa iyalen su abubuwan jin dadin rayuwa.Shin ba abu mai kyau bane iyalen sa suma su bada nasu gudunmawa ga tafiyar da gida?
Domin a zamanin da muke ciki a yanzu in magidanci na bukatar ya'yan sa su sami nagartattcen ilimi sai ya kai su makarantu masu zaman kan su .Haka ma batun kiwon lafiya da sauran al'amurran tafi da rayuwa na yau da kullum. Ga halin rasa aiki ko sana'a da dubban magidanta suka sami kan su bisa sauye sauye a manufofin gwamnati ,shi ke nan in maigida ya sami kansa cikin tsaka mai wuya sai iyalen sa gaba daya su tagayyara?A kullum muna cin karo da gungun mata da ya'yan su masu tsaida mutane a kan hanya suna neman taimako ko in ce bara,da dubban kananan yara (musamman mata )da ake turo su daga kauyuka domin a'ikatau a gidaje a birane.
Sannan wani babban matsalar da ake fama da ita da kusan kowa ya tsuke bakin sa shine na matsalar yawan Zaurawa .Kusan yadda ake yawan aure ,haka ake yawan sakin matan ,ko kuma mazajen su gudu su bar matan! Me ke kawo yawan sakin mata a yanzu?Koma menene dalilan akwai bukatar samin bakin warware wannan matsalar na yawaitan Zaurawa.
Kungiyoyin mata da kungiyoyin mutunta hakkin yan'adam da matan shugabanni a kowane mataki bisa jagorancin Shugabanin addini ya kamata suyi kokarin ganin ana martaba mata tare da bi masu hakkin su yayin da mazajen su zasu sake su .A wannan lokacin na tsarin dimokaradiyya akwai bukatar neman majalisun dokoki daga jiha har tarayya su yi dokokin da dole in magidanci zai saki matar sa sai a kotu da biyan ta wasu makudan kudade da zai ishe ta tafi da rayuwar ta har ta sake aure. Mafi yawan masu sakin matan su nada ketar ganin matan su tagayyara su kuma rasa tudun dafawa .Haka kuma sau dayawa akan sha wahala da mata ana zaman aure ,amma da zarar walwala tazo sai mazajen su, su hura masu wutar kiyayya har sai an rabu,kiri kiri suna ji suna gani dadi yazo za'a ci babu su. Sannan ga maza marasa tausayi da suke sakin matan su in wata laluran rashin lafiya ta same su dan kawai kada su kashe kudin su wajen neman magani.Wasu mazan kuma dan hannun su da shuni sai su auri mata su sake su in suka cimma burin su !
Lokaci yayi da matan Hausawa zasu hada kafada da sauran matan kasashen da suka cigaba musamman na kasashen Musulmi inda suke da dama kamar kowa ta wajen samun ilimi mai zurfi da damawa asha dasu a harkokin kasuwanci da kimiyya da siyasa.Amma wannan damar ba zata samu ba sai sun yinkuro da kan su domin ganin cewa ana basu damar da addinin su ya basu ,tare da juya baya ga duk wata al'ada da zai tauye cigaban su a rayuwar zamanin mu na yau domin su bada tasu gudunmawar ga bunkasar tattalin arziki da cigaban Arewa da Nijeriya.

Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com
http://shehuchaji.blogspot.com/

Thursday, 17 May 2007

Memo to Nigerian Masses

With the amalgamation of Northern and Southern protectorates as one entity named Nigeria in 1914, the Nigerian masses have been giving the highest contribution to the growth and development of Nigeria. Masses contributed their quota in terms of monies they paid as taxes, cheap labour for production and even their lives when Nigeria was at the brink of disintegration.

During the colonial period the Nigerian masses were exploited by the British imperialist colonial masters through large scale production of agricultural products such as the pyramids of groundnuts in Kano, mass production of cotton, cocoa, palm oil, cassava e.t.c which the British determine their prices instead of them to determine the price of their own products for shipment to Britain. Masses provided the almost free labour that railway was constructed to facilitate transport of goods and services to the sea for export. They paid taxes on everything from paying taxes on themselves, members of their families and on almost everything they owned such as cattle, livestock, farmland and household property. This exploitation was perfected through the collaboration of traditional rulers and middlemen in the name of indirect rule.

When Nigeria obtained independence in 1960, the Nigerian masses had the hope that their condition of living would improve as their fellow blacks were to be at the helm of affairs. But what did the masses have in return for their sufferings and exploitation during the colonial period? The new ruling class instead of bringing the nation together to harness the abundant human and natural resources that the nation was blessed with, they were only concerned with how they could garner more influence and power though laying the foundation of tribalism, nepotism, regionalism and religious differences.

Ethnicity and regionalism reached zenith in 1966 when Igbo military officers toppled the first republic and paving the way to Nigerian civil war that consumed the lives of more than one million Nigerian masses on both sides of the conflict . The principal actors of the Nigerian civil war fled when they saw outright defeat leaving the used masses to face the wrath of the advancing victors to safe haven abroad and are today living and enjoying.

The Nigerian Masses have no friends, comforters, sympathizers and helpers .The ruling elites, either military or civilians, have always collaborated with traditional rulers, the clergy and business community to inflict more hardship on the masses through implementation of policies such as SAP, increase in prices of petroleum products and deregulation of the economy. Masses are left to suffer alone as whenever they tried to rise to resist such policies the traditional rulers and clergy men will be at work preaching peace and Almighty wrath on whoever tries to cause violence. They never speak on behalf of the masses to the ruling class that the masses are suffering and the government should scrap those inhuman policies.

Masses in Nigeria are used to turn against each other through preaching of intolerance and hate by politicians and clergymen in the name of religion. Thousands of innocent masses have been murdered in various religious conflicts over the years in various parts of the country .The elites that engineer such religious conflicts never send their children to participate actively in any spate of violence.

Ethnicity have been used also to make masses kill one another when some political elites lose in power game , they use the ethnic card to seek relevance and recognition .Such ethnic conflicts have also led to thousands of Nigerian masses to lose their lives and turn refugees in their own country .

The political class and their cronies have mutual understandings in their companies board meetings where you will find them together irrespective of tribes, regions or religions .They all have the common interest of exploitating and stealing the nations wealth and only complain when they were edged out or can’t fulfill personal agenda of control and distribution of national or state resources .
In political thuggery, rigging and manipulation of elections results, the masses are used by giving them peanuts amount of money being which hardly reaches beyond swearing those benefactors of stolen and rigged mandate into office.

When will Nigerian masses be aware that they have a common enemy? When will they realize that they are being used by some cabals to achieve their personal interests and ambitions in the name of ethnicity, regionalism and religion? When will they realize that when such cabals are in corridors of power they never complain of being marginalized, only when they are outside the corridor of power they start the struggle on the pretext that their tribes, regions and religion have been marginalized?

When Northerners were at the helm of affairs what special privileges did the common Northerner benefit from the government? Presently with a Southerner and a Yoruba at the helm of affairs, what special benefits and privileges are the common Southerners and the Yoruba in particular enjoying from the government? Which parts of the country before and presently are there that do not have traces of abject poverty, bad roads, in equipped hospitals, unemployment, insecurity, lack of portable water, constant electricity, affordable shelter and looting of their treasuries?

The ruling elites and their collaborators in traditional institutions and men of religion have the same trademark as they live in reserved quarters with red roofs , move in convoy of exotic cars with hefty bodyguards behind them. Some of them have become so fat and large that they hardly move except like anti-natal mothers.

Nigerian masses have to collectively come together, irrespective of tribe, region and religion, to fight for their common good and future. If they continue to allow themselves to be brainwashed in such issues of tribe, region and religion, the cancerous elites will continue to inflict continuous hardships and cycle stealing of our national wealth.

Mutual understanding, tolerance and respect of each other’s way of life and beliefs is what the Nigerian masses need to move this nation forward. Destiny has joined us together as Nigerians. Nigeria has to remain as a common entity as no tribe , region or religion can live on it’s own .

Unity brings power and if Nigerian masses continue to be used not to attain unity , the sufferings of today as that of yesterday will be inherited by the unborn children of the masses .The earlier they realize the importance and value of unity the better .



Shehu Mustapha Chaji

wohoho yaushe talakawan Nijeriya zasu gane ne?

Tun a shekarar 1914 da turawan mulkin mallaka suka hada kudancin da arewacin wannan kasa da suka rada wa suna Nijeriya talakawa ke bada gudunmawa mafi tsoka wajen cigaban wannan kasar. Gudunmawar su ta kasance ta hanyoyin biyan harajai ,aiki kusan na bauta da kuma rayuwar su a lokacin da Nijeriya ta fuskanci barazanar wargajewa.

A lokacin mulkin mallaka turawan Ingila sun bautar da talaka ta hanyar samar da amfanin gona kamar dalar gyada ta Kano,noman auduga ,koko ,manja ,rogo da sauran su. Turawan mulkin mallaka suke sawa albarkatun gonar da talakawa suka noma farashi maimakon wanda ya noma ya sawa kayan sa farashi domin jigila zuwa kasar Birtaniya.Talakawa su suka yi aikin gina titin dogo domin samar da sifirin da za’ayi dakon kaya zuwa bakin teku. Sukan biya haraji kan komai daga kawunan su, iyalan su da abubuwan da suka mallaka kamar dabbobi ,gonaki da kayayyakin da suka mallaka . Wannan zalunci ya samu tabbata ne tare da hadin kan masarautun gargajiya da yan koren turawa da sunan mulkin cin gashin kai.

Lokacin da Nijeriya ta samu yancin mulkin kai a shekarar 1960 , talakawa na ta murnan cewa al’amura zasu canza tunda yan’uwan su bakake zasu kasance masu gudanar da harkokin mulkin wannan kasa. Amma mai talakawa suka samu sakamako game da wahalar da zalunci da suka fuskanta a hannun turawan mulkin mallaka ? Sabbin shugabanni da aka samu maimakon su maida hankali su ga hada kan kasa domin cin gajiyar dinbin arzikin albarkatun kasa da Allah yayi wa wannan kasar baiwa da ita sai ya kasance sun maida hankalin su gun kokuwar dafe madafan iko da samun girma wanda ya kaisu da fara haza harsashin kabilanci , son kai , bangaranci da nuna banbancin addini.

Kabilanci da bangaranci ya kai matuka a shekarar 1966 da wasu sojojin kabilar Ibo suka gagoraci juyin mulkin da ya hambarar da gwamnatin jamhuriya ta farko wanda sakamakon haka ya kai Nijeriya da fadawa cikin yakin basasa wanda ya janyo halakar dubban talakawa daga kowane bangare na Nijeriya. Jagororin wannan yaki da suka fuskanci shan kasa suka tsere zuwa kasashen waje suka bar talakawan da suka ingiza kuma a yau suna raye suna holewar su.

Talakawan Nijeriya basu da abokane, masoya , mataimaka da masu tausaya masu na hakika. Masu mulki sojojin su da farar hula sun kasance masu hada kai da masarautun gargajiya , malaman addini da manyan yan kasuwa domin kara jefa talaka cikin wahala ta hanyoyin mara wa manufofin gwamnati daka gallazawa talaka kamar janye tallafin gwamnati a abubuwan more rayuwa da karin kudin man fetur da gangoginsa .An bar talaka cikin bakar wahala da kuncin rayuwa kuma duk yayin da suka so su motsa domin neman wa kansu yaci sai masarautu da maluman addini su shiga dakufar da talakawar da cewa Allah ya la’anci mai tada fitina. Basa sanar da gwamnati cewa lallai talakawa na cikin wahala dan haka gwamnati ta taimaka ta janye manufofin ta da zai jefa talaka cikin karin wahala da kunci .

Koda yaushe yan siyasa da maluman addini sun kasance cikin ingiza talakawa suyi ta rikici a tsakanin su da sunan addini. Dubban talakawa sun rasa rayuwar su a sakamakon fadace-fadace da sunan addini a jihohi da dama na kasar nan. Yan siyasa da malaman addini dake ingiza talakawa rikici a tsakanin su basa taba tura yayan su su kasance a sawun gaba yayin irin wadanan tashe-tashen hankula.

Ana kuma amfani da kabilanci wajen ingiza talakawa su kashe junan su . Duk yayin da wasu masu fada aji suka rasa madafen iko sai su fake da zancen kabilanci da bangaran ci wajen kokarin samu damar fada aji . Rigin-gimun kabilanci yayi sanadiyar dubban talakawa sun rasa rayukan su tare da maida wasu dubbai sun zama masu gudun hijira a cikin kasar su ta haihuwa.

Masu mulki da yan koren su sun kasance masu fahimtar juna a kamfanonin su na hadin gwiwa inda zaka same su tare ba tare da banbancin kabila, bangare ko addini ba . Sun kasance masu manufa daya na tara dukiya ta kowace hanya . Basa korafi sai yayin da suka kasa cimma manufar su na juya da sarrafa dukiyar kasa ko ta jiha.

A bangar siyasa , magudi da murda-murdan zabe da talakawa ake amfani dasu ana basu dan abunda ba zai ishe su kashewa ba tun kafin a rantsar da wadanda suka ci gajiyar magudin zabe.

A yaushe talakawan Nijeriya zasu fahimci cewa suna da makiya guda? A yaushe talakawa zasu fahimci cewa ana amfani da su ne dan biyan bukatar wani ko wasu mutane dake kokarin cimma burin su suna fakewa da sunan kabilanci , bangaranci da addini? A yaushe zasu fahimci cewa yayin da wadannan mutane ke farfajiyar mulki basa zancen an danne kabilarsu , yankin su ko addinin su. Sai yayin da suka rasa madafan iko sai su shiga gwagwarmayar an danne yankin su, kabilarsu ko addinin su .

Yayin da yan’arewa ke mulkin wannan kasar wacce dama ta musamman talaka dan arewa yake samu daga gwamnati?A yanzu da dan kudu kuma bayarbe ke mulki wane dama ta musamman yan kudu da yarbawa ke samu daga gwamnati? Wane bangare ne na Nijeriya ba’a fama da talauci, rashin aikin yi, rashin ruwa , wuta , tituna masu kyau , rashin tsaro, kyawawan muhalli da sace dukiyoyin su?

Masu mulki da yan koren su a gidajen sarautu da maluman addini sun kasance da kamanni guda inda zaka same su suna zaune a kebabun unguwanni da manyan gidaje masu jan rufi , suna tafiya a jerin gwanon motoci masu tsada tare da jibga-jibgan masu gadin su. Wasu cikin su har sun yi kiba da tumbi kamar mace mai cikin wata tara.

Lokaci yayi da talakawan Nijeriya zasu hada kansu ba tare da kyamar juna ba saboda banbancin addini , yanki da kabila domin samar wa kansu rayuwa mafi kyau da ingaci . In suka yarda aka cigaba da amfani dasu wajen raba kansu kan kan banbancin kabila , yanki da addini masu mulki da yan koren su zasu cigaba da azabtar da talaka da sace masu dukiyar kasa.

Fahimtar juna , girmama juna da ganin mutuncin juna shine abubuwan da talakawan Nijeriya suke bukata wajen cigaba da dorewar kasar mu Nijeriya. Kaddara ta riga ta hada mu mun zama yan kasa daya kuma wata kabila, ko yanki ko addini ba zata iya dorewa ita kadai ba ba tare da chudanya da yar’uwarta ba.

Hadin kai ke kawo karfi in kuma talakawan Nijeriya suka bari aka cigaba da raba kan su to wahalar yau kamar ta jiya zata tarar da yayan mu da zasu zo nan gaba, Fahimtar hadin kai da girmama juna shine zai ciyar da kasar mu gaba a cikin kasashen duniya.

Haza wassalam nine

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Janar Babangida na cikin tsaka mai wuya

A shekara mai zuwa waton 2007 Nijeriya zata sami sabon shugaban kasa mai cikakken iko yayin da wa'adin shugaba Obasanjo zai kare. Cikin tsahun gaba -gaba na masu neman shugabancin Nijeriya a shekara ta 2007 shine tsohon shugaban mulkin soja Janar Ibrahim Babangida.
Tun lokacin da Babangida ya furta cewa zai tsaya takarar shugabancin wannan kasar masoyan sa da masu adawa dashi suke kai gwauro su kai mari kan dacewar sa ko a'a kan ya sake dawowa bisa kujerar mulkin wannan kasar.Ta bangaren gwamnati mai ci a yanzu manazartan harkokin siyasa suna ganin cewa bashi da goyon bayan shugaba Obasanjo saboda yadda gwamnatin sa take ta kokarin ganin tayi wa Babangida kofar raggo ta hanyar kama dan sa Mohammed Babangida kan tuhumar mallakar kashi ashirin da hudu na kamfanin wayar sadarwan globacom, da bincike kan shari'ar kashe marigayi Janar Mamman Vatsa , da bayyana rahoton Okigbo kan yadda kudade fiye da dala biliyan goma sha-biyu sukayi batan kai na raran man-fetur da aka samu lokacin yakin tekun fasha.
Masu goyon bayan Janar Babangida suna ganin cewa a lokacin sa ya samar da cigaba ta fannoni da dama kamar su hukumar samar da aikin yi (N.D.E),Bankin talakawa (People's Bank),hukumar kare haddura(FRSC),hukumar raya karkara (DEFRI),hukumar wayar da kan matasa (MAMSA)gina tagwayen hanyoyi kamar na Kaduna zuwa Kano,kafa jam'iyyu da basu kudaden tafiyar dasu,hukumar wayar da kan mata (Better Life) da sauran su .Suna ganin cewa in har Babangida ya sake dawowa bisa kujerar mulki to za'a sami cigaba fiye da wanda aka samu a lokacin da yake mulki irin na kama karya ta soja.Kuma suna ganin cewa inshi ya bata to a bashi dama yazo ya gyara.
Akwai masu ganin cewa kafin ma Babangida ya fito dan tsayawa takara ana da bukatar yayi wa Yan-Nijeriya cikakken bayanai game da irin rawar da gwamnatin sa ta taka wajen soke zaben June 12 , yadda akayi da sama da dala biliyan goma sha-biyu na rarar man fetur , kashe Dele Giwa ,hatsarin jirgin saman hakulas dauke da sojoji a legas, gaskiyar zancen yunkurin juyin mulkin marigayi Mamman Vatsa da kashe shi , shigar Nijeriya kungiyar O.I.C da maida huldan jakadanci da kasar Isra'ila, da kuma uwa uba karbo bashi daga bankin duniya wato I.M.F da daura Nijeriya bisa tafarkin S.A.P da ake ganin shi ya karya darajar naira ta kuma jefa Nijeriya a halin kakani-kanin da take ciki a yanzu.
Amma babban abun tambaya gashi Babangida da magoya bayan sa shine a yaushe shi janar din ya amince da kuma yarda da tsarin dimokaradiya?Domin a lokacin sa ya kawo tsare-tsaren da yayi wa dimokaradiya targade ko kuma ace ya karyata. A lokacinsa ne jam'iyyun N.R.C da S.D.P suka gudanar da zaben fidda gwani wanda Malam Adamu Ciroma a jam'iyyar N.R.C da marigayi Janar Shehu Musa Yar'aduwa ya lashe a jam'iyyar S.D.P sai kawai ba tare da wani muhimmin bayani ba ya rushe zaben nasu.
Haka ma Babangida yasa yan-siyasa da al'ummar kasa sake shiryawa da fitowa sabon zaben da aka tsara na shugaban kasa a inda Alhaji Bashir Tofa na jam'iyyar N.R.C da marigayi Cif M.K.O Abiola na jam'iyyar S.D.P suka tsaya takara . Ana cikin bada rahotannin sakamakon zaben kwatsam sai Babangida ya soke zaben ba tare da wani kwakwaran dalili ba. Rigingimun da suka biyo baya shi ya tilasta masa sauka kan mulki bada shiri ba bayan shekara takwas yana mulki.
Soke zaben June 12 ya jefa Nijeriya cikin wani yanayin rikici da tashin hankalin siyasar da tun yakin basasar Nijeriya ba'a taba fuskantar irin wannan yanayi ba. Tirjewan da kabilar Yar'bawa sukayi na an soke zaben da dan'uwan su ya dauki hanyar lashewa yasa a zaben 1999 aka barwa Yar'bawa su kadai suka tsaya takara waton Cif Olu Falae da Cif Olusegun Obasanjo. Sanin kowa ne yadda Janar Babangida ya taka rawa wajen ganin cewa Cif Obasanjo shi ya lashe zaben.
A shekara bakwai da Shugaba Obasanjo yayi yana mulki sau nawa Janar Babangida ya fito domin kare talakawa daga manufofin gwamnatin da suke takura talaka da jefa talakawa cikin halin ni yasu? Shin da yan-arewa suke ta koken cewa wannan gwamnatin na danne su Babangida ya fito ya samar masu sauki?
Janar Babangida ya shedawa Yan-Nijeriya cewa babu gudu babu ja da baya zai fito takarar neman Shugabacin kasa a zaben 2007 . Masu nazari kan harkokin siyasa nata tsokaci kan rawar da Janar din zai taka wanda zai iya kai shi ga samun nasara ko faduwar sa a zabe. Tun zangon farko na wa'adin Shugaba Obasanjo masoya da magoya bayan Babangida suke ta kira gareshi ya fito amma Janar din yayi bayanin cewa shi ba zaiyi takara da Shugaba Obasanjo ba. To yanzu da Shugaba Obasanjo ba zai tsaya zabe ba a shekarar 2007 kuma a yadda Yan-Nijeriya suke tsammani na cewa Shugaba Obasanjo zai rama wa kura aniyar ta sai gashi alamu suna ta nunawa cewa Obasanjo ba zai goya wa Babangida baya ba.
A wannan yanayin da Janar Babangida bashi da goyon bayan Shugaba Obasanjo ga yan takara biyu masu karfi da tasiri wato mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar da Janar Muhammadu Buhari lallai Janar Babangida nada jan aiki wajen lashe zaben 2007 .
Ba shakka Janar Babangida nada tasirin gaske a siyasar wannan kasar da kuma masoya da mogoya baya masu yawa. Ya rage ga shi Janar din ya san yadda zai tallata kansa ga Yan-Nijeriya su mara masa baya domin sake samun damar dawowa ya mulki Nijeriya a tsarin dimokaradiya. Manufofin sa da zai aiwatar na iya sa Yan-Nijeriya su amince dashi ya kaiga ya lashe zaben 2007 .
Masoya da magoya bayan Janar Babangida har ila yau na bukatar cikakken bayani kan lallai zai fito takara ko a'a domin ga dukkanin alamu har yanzu yana jan kafa wajen tsunduma cikin harkokin siyasa da zai kaishi ga tsayawa takara. Kuma ga fitowar Janar Aliyu Gusau takarar shugaban kasa shima wanda ake ganin tare suke kuma in har da gaske Babangida zai fito to Janar Gusau ba zai tsaya takara ba.
Batun jam'iyyar da Janar Babangida zai tsaya ma har yanzu bai bayyana ba duk da cewa shi sannan dan jam'iyyar P.D.P ne. Takarar sai da gwani na jam'iyyar tasa da alamun tana yi masa kwarjini wanda yasa ya raba kafafuwansa a jam'iyyu masu dama. Koda yake jam'iyyar N.D.P ta rigaya ta bashi damar tsayawa a matsayin dan takaranta na shugaban kasa , amma ko jam'iyyar zata karbu har ta kaishi ga cimma burinsa to al'amurran siyasa kafin zaben 2007 kadai zai iya tabbatar da haka.
Wani abin murna da farin ciki shine cewa fitowar ire-iren su Janar Babangida na tabbatar da daurewar tsarin dimokaradiya a wannan kasa wanda mulkin soja ya ja mata tsaiko ga cigaba ta fanin siyasa , zamantakewa da bunkasar tattalin arzikin kasa .
Zaben 2007 ya zama kalubale ga Janar Babangida domin ya rigaya ya furta cewa lallai zai fito . Dole cikin abubuwa uku a sami daya , kodai yaki fitowa takara wanda zai tabbatar da zancen manazartan harkokin siyasa cewa Janar Babangida matsoraci ne a fagen siyasa na gwagwarmayan neman al'umma ta mara masa baya ya kaiga darewa kan kujerar mulkin Nijeriya a tsarin dimokaradiya. Nabiyu, in har ya fito takara aka kada shi a zaben to alkadarinsa ta karye a yadda al'umma suke ganin sa a wani dodon bango mai bada tsoro. Na uku , in ya fito takara har ya kaiga lashe zaben 2007 to ya tabbatar wa al'ummar Nijeriya da duniya gabaki daya cewa shine mutumin da yafi tasiri a siyasar wannan karni ba'a Nijeriya kadai ba har ga Afrika gabaki daya . Kuma wannan shi zai bashi babbar dama na gyara sunan sa a tarihin siyasar Nijeriya domin mutanen Nijeriya da dama suna ganin shine ya jefa Nijeriya a halin da ta tsinci kanta a ciki har yanzu.
Ina mai kira ga Janar Ibrahim Babangida da ya tsuduma cikin harkokin siyasar zama shugaban kasa a 2007 ba dan komai ba , dan wannan wata dama ce da zai fito yayi wa jama'ar Nijeriya kwararen bayanai da zasu gamsu kan cewa wasu abubuwan da auka faru yayin da yake kan mulkin Nijeriya alheri ne ga kasan.Kaman yadda Janar din yayi bayani da kansa a wata hira da sashen hausa na B.B.C lokacin yaki da tazarce cewa yan-majalisa su sani suna da ya'ya wanda in sukayi abunda jama'a basa so to zasu barwa ya'yan su abun fadi . Lallai tun Janar din nada rai da lafiyar sa to ya fito karara ya fadi dalilan da yasa ya aiwatar da wasu manufofi wanda a yau shi kadai akasa a gaba sanin cewa akwai majalisar koli ta kasa (A.F.R.C) a lokacinsa wanda dukkan matsayin da ya dauka sai da amincewa da yardan su .
Dabara ta rage game shiga rijiya , mu talakawa fatan mu shine Allah ya bamu shugaba nagari wanda zai fidda talaka daga halin kakani-kanin da ya sami kansa a ciki . Gashi Janar Babangida in har yana da kyakyawan manufa da buri na inganta da cigaban talaka da Nijeriya sai muce Allah ya bashi sa'a.

Haza wassalam Nine

Shehu Mustapha Chaji

shehuchaji@yahoo.com

KO GWAMNA SHEKARAU ZAI MAIMAITA?

Jam’iyyar PDP ita ta lashe zaben 1999 lokacin da sojoji suka mika mulki ga gwamnatin dimokaradiya a jihar Kano . Amma sai reshe ya juya da mujiya a zaben 2003 inda Malam Ibrahim Shekarau karkashin inuwar jam’iyyar ANPP mai adawa ta karbe mulki a hannun Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso na jam’iyyar PDP.

Gwamna Ibrahim Shekarau ya sha fama da gwagwarmaya kafin ya zama dan takarar jam’iyyar ANPP a jihar Kano . Saboda wanda jam’iyyar ta tsayar da farko Alhaji Ibrahim Al-Amin Little bai sami amincewar tsofin yan jam’iyyar ba inda sai da sukayi kullin da aka maye shi da Malam Shekarau a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar ANPP. Kuma faduwa tazo daidai da zama inda yaci gajiyar umarnin da Janar Muhammadu Buhari ya bayar ga magoya bayan sa na a zabi “ANPP SAK”.

A shekaru kusan hudu da yayi kan kujerar mulki Gwamna Shekarau ya aiwatar da aiyuka daban daban kamar samar da aikin yi a ma’ikatun gwamnati , koyar wa matasa sana’oi , kafa hukumomin da zasu kula da Shari’a kamar zakka da kumusi, Hisba ,A daidaita sahu da hukumar Shari’a, ya kuma gina sababbin ajujuwa da makarantu , bawa yaya mata ilimi kyauta,kari kudin tallafi ga dalibai a manya makarantu , karin albashi ga ma’ikata, bayar da abun buda baki kyauta da watan azumi, samar da motocin haya daban daban ga mata da maza ,d.s .

Daga bangaren yan’adawa suna ganin cewa bawani abun azo a gani da Gwamna Shekarau ya aiwatar na cigaba da bunkasar jihar Kano . Sunce gwamnatin sa ta karbi biliyoyin nairori daga gwamnatin tarayya a matsayin kason ta amma babu aiyuka da zaka iya nunawa a kasa cewa ga inda akayi aiyuka da kudaden . Sannan kuma sunce yana shekara biyu bias karagar mulki karbi fiye da dukkan kudin kason kasa da Gwamna Kwankwaso ya samu a shekara hudu.

Magoya baya da masoyan Gwamna Shekarau tun a bara suka yi ta kira a gareshi da ya sake neman komawa bias karagar mulki a wa’adi na biyu sanin cewa shi Gwamna Shekarau da kansa ya shedawa Kanawa cewa shi wa’adi guda kawai zai yi domin shi a kamus dinsa ta siyasa babu tazarce . Gwamna Ibrahim Shekarau dai ya fito ya amsa kirasa na sake neman komawa gidan gwamnati a karo na biyu da magoya bayansa kewa lakabi da “tamaimaita” sabanin kalmar tazarce da aka fi sani.

Shin Gwamna Shekarau zai cimma burin sa na sake maimaitawa?Shin Shekarau zai zama mutum na farko a tarihin siyasar Kano wanda zai yi mulki har wa’adi biyu?Shin yanayin siyasa a shekarar 2003 dai dai yake da na yanzu? Samun amsoshin wannan tamboyoyin kadai shi zai iya nuna ko Gwamna Shekarau zai maimaita ko a’a .

Ta bangaren jam’iyyun adawa kamar su PDP, AC, PSP wanda masu nazari kan harkokin siyasa suna ganin cewa zasu taka muhimmiyar rawa wajen kokarin gadar da wanda zai maye Gwamna Shekarau a zabe mai zuwa . Jam’iyyar PDP da aka karbe mulki a hannun ta a 2003 ta cika ta batse day an takara masu son karbe wa PDP mulkin ta a hannun ANPP. Fittatu daga cikin su sune Arc. Aminu Dabo , Alhaji Ibrahim Al-amin Little , Alhaji Salisu Buhari tsohon kakakin majalisar wakilai , Dr.Abdullahi Ganduje , sai shi tsohon gwamna wato Engr Rabi’u Musa Kwankwaso da magoya bayansa suka saya masa form na takara d.s . Daidaituwa da zaben gaskiya gun fidda gwani na iya samara wa jam’iyyar PDP dan takarar gwamna na gari da za’a kai ruwa rana dashi a zaben na 2007 a jihar Kano .

Jam’iyyar A.C wanda mafi yawa daga cikin ya’yanta da shugabanin ta kaura sukayi daga jam’iyyar PDP da ANPP a jihar Kano . Jam’iyyar nada jiga-jigan yan siyasa irin su tsohon gwamnan jihar Kano Dakta Abubakar Rimi , tsohon minister Alhaji Musa Gwadabe , tsohon kakakin majalisar wakilai Alhaji Ghali Umar Na’abba da Hajiya Naja’atu Bala Mohammed d.s . Fittatun yan takarar gwamna a jam’iyyar ta A.C sune Alhaji Sule Ruruwai da Alhaji Ghali Umar Na’abba da magoya bayansa ke matsawa ya fito takara shima . Duk wanda jam’iyyar ta tsayar ana ganin cewa lallai zai taka muhimmiyar rawa a zaben 2007 saboda sanin makaman aiki da suka yi .

Ta bangaren jam’iyyar PSP kuma wanda badan Janar Buhari yayi umarnin da’a zabi ANPP SAK ba to da ana tsammanin jam’iyyar ita zata kafa gwamnati a shekarar 2003 a jihar Kano . Dr. Yakubu Danhassan tsohon akanta janar a gwamnatin Gwamna Kwankwaso kuma na hannun daman sa sun raba gari saboda bukatar shi Danhassan din na shima ya gaje kujerar Gwamna Kwankwaso a zaben 2003 . Yayi matukar farin-jini da samun karbuwa kafin guguwar ANPP SAK ta dushe tauraron sa . Shima yana ta shirye-shiryen tallata kansa ga Kanawa su bashi dama ya zama gwamnan su karkashin jam’iyyar sat a PSP.

Lallai Gwamna Shekarau nada jan aiki inda gasket yake na yunkurinsa na komawa a karo na biyu. Ga rigin-gimun cikin gida ta jam’iyyar sat a ANPP inda ta dare gida biyu ko wace bangaren na ikirarin cewa itace ta halas . Ga zarge-zargen da akeyi wa Gwamna Shekarau na cewa sun riga sunyi hannun riga da Janar Buhari musamman rawan da ake zargi shi Shekarau ya taka wajen ganin cewa yan takara masu goyon bayan Janar Buhari basu kai labari ba a zaben fidda shugabannin jam’iyyar ta ANPP a Abuja kwanakin baya.

Yan siyasar jihar Kano suna da wani canfi na cewa ba’a mulkin Kano sau biyu . Suna cewa a tarihin siyasar Kano ba’a taba samun wanda yayi mulki ya sake nema ya samu ba. Suna kawo misalai da tsohon Gwamna Abubakar Rimi wanda duk da farin-jinin sa Marigayi Alhaji Sabo Bakin-Zuwo ya kada shi , Arc. Kabiru Gaya tunda ya bar mulki yake ta yunkurin sai ya koma amma har yanzu burin sa bai cika ba . Haka ma tsohon Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso hakansa bata cimma ruwa ba. Ko Gwamna Shekarau zai karya wannan canfi da ake fada na kasa samun wa’adi na biyu ?Abun da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa .

A shekarar 2003 rundunar da ta hada kai takai Shekarau ga gidan gwamnatin jihar Kano ta daddare .Gwamna Shekarau ya rigaya ya raba rana da yan’jam’iyyar tasa da suka mara masa baya a zaben 2003 kamar Alhaji Haruna Ahmadu Dan-Zago da a yanzu ya farraka da nashi bangaren na jam’iyyar a jihar Kano.Hajiya Naja’atu Bala Mohammed wanda itace ta samara da kalmar ANPP SAK ta fice daga jam’iyyar zuwa AC ,Janarorin da suka mara masa baya irinsu Janar Bashir Magashi shima ya kama gaban sa , shi kuma Birgediya Janar Halliru Akilu zai mara wa uban gidansa wato Janar Babangida baya wanda a yanzu yana cikin jam’iyyar PDP . Malaman da suka mara masa baya domin ya aiwatar da Shari’ar Musulunci suma sun zarge shi da kasa aiwatar da Shari’a yadda ya kamata har sun ajiye mukamman su a gwamnatin sun fice .

Uwa uba Gwamna Shekarau da Janar Buhari sunyi kalamai masu banbanci da juna a hirar da akayi dasu a gidan rediyon BBC inda Janar Buhari yace anyi magudi a zaben fidda shugabannin jam’iyyar ta kasa shi kuma Gwamna Shekarau y ace anyi zabe na gaskiya . Amma masu nazari kan harkokin siyasa na ganin cewa kowannen su na bukatar juna don cimma burikan su wato Janar Buhari dan lashe zaben fidda gwani na shugaban kasa a jam’iyyar ANPP shi kuma Gwamna Shekarau dan samun goyon bayan sa dan sake komawa karagar mulki .

Rana dai bata karya sai dai uwar diya taji kunya , Ko Gwamna Shekarau zai maimaita ?Lamari ne da Kanawa zasu tantance a zaben 2007 in sun gamsu da aiyukan sa . Lallai in Gwamna Shekarau ya lashe zaben 2007 ya maimaita to lallai ya kafa tarihi da ba masu adawa dashi kunya a fagen siyasa .

Haza wassalam

Shehu Mustapha Chaji

Saturday, 12 May 2007

BANKWANA DA SHUGABA OBASANJO

A kwana a tashi rananar 29 ga watan mayu na wannan shekarar Shugaba Olusegun Aremu Obasanjo zai kamala mulkin sa na tsawon takwas a karagar mulkin Nijeriya , wanda a wannan ranar ne zai mikawa Alhaji Umaru Musa Yar’adua mulki a matsayin zababbaben shugaban kasa.

Yan Nijeriya zasu yi kewar Shugaba Obasanjo bias mahangar da suke kallon sa.Ya kasance hadari sa gaban ka inda kake so , domin duk abinda ransa ya biya masa ko ana ha maza ha mata sai ya aiwatar dashi.

An sami cigaba ta fannoni da dama a shekarun da yayi bias mulki .A lokacin mulkin sa ne wayar tafi da gidan ka ya zama ruwan dare ,sabanin shekarun baya da wayar sadarwa sai masu hannu da shuni. An aiwatar da manufofin sauye-sauye daban daban musamman a fanning tattalin arzikin. Sabbin manufofin sun karfafa bankuna da sabon tsarin fansho da Karin albashi da biyan basusukan da suka yi ma Nijjeriya katutu. Shugaba Obasanjo ya kuma kafa hukumomin yaki da cin hanci da almudahana ta hanyoyin kirkiro hukumomin EFCC da ICPC wanda a lokacin mulkin sa ne manya jami’an gwamnati har da babban sufetun yan’sandan Nijeriya Tafa Balogun suka fuskanci shari’a bias tara dukiya ta hanyar haram. An kuma sake fasalin babban birnin tarayya Abuja domin ta kasance cikin manyan biranen duniya da gina tashoshin bada wutar lantarki da kuma bada kwangilar gina tagwayen hanyoyi da sabon tashoshi da jiragen kasa da sauran su.

Shugaba Obasanjo ya kuma kasance wanda a lokacin mulkin sa duk da dai shi ba Musulmi bane, jihohi da dama suka sami damar aiwatar da Shari’ar Musulunci ba tare da fuskantar wata tsangwama ba daga gwamnatin tarayya. Ya kuma kasance shugaba mai girmama addinan talakawan sa inda a watan azumi ,dashi ake azumi. Bai kuma mika wuya ga kasashen da suke yaki da ta’addanci ba wajen shirya makircin da za’a yi farautar Musulmi ba da sunan yan’atadda bane .

Amma ga talakawan Nijeriya da yan ‘adawa suna ganin cewa ba’a taba samin gwamnatin da ta jefa talakawa cikin halin kakanikayi ba kamar lokacin mulkin Obasanjo. Kamar yadda Janar Muhammadu Buhari ya sha fadin cewa tun lokacin aka samar da Nijeriya a shekarar 1914 babu gwamnatin da ta sami kudin shiga kamar gwamnatin Obasanjo , sannan babu lokacin da talauci da fatara yayi wa al’umma katutu kamar lokacin gwamnatin Obasanjo.Sannan kasar bata taba shiga halin rashin tsaro ba kamar a wannan lokacin inda dubban jama’a suka rasa rayukan su a tashe tashen hankulan addini da kabilanci da fashi da makami da kisan gillar da akayi wa fitattun mutane.

Duk da makudan kudaden da gwamnatin sa ke fadin ta kasha kan samar da wutan lantarki , kasar ta kasance cikin duhu har ta kai ga kamfanoni da masana’antu da dama sun durkushe. Haka ma babu ingantattun hanyoyi da tsaftatacen ruwan sha , ga rashin aikin yi da Koran dubban ma’aikata daga aiki wanda ya jefa dubban mutane majiya karfi zaman kasha wando. Karin kudin man fetur da dangogin sa babu kaukautawa ya haddasa tsadan rayuwa da kara jefa talaka cikin halin matsi da da gwamnatin Obasanjo keyi kusan kowane shekara.
Kan batun yaki da cin hanci da rashawa wasu masu nazarin harkokin yau da kullum na ganin cewa a baki kawai gwamnatin Obasanjo ke yaki da cin hanci da rashawa. Saboda suna ganin akwai wadanda suka zama yan lele sa ,duk da korafin da ake na a bincike su amma ya toshe kunnen sa ,amma sai wanda suka kasance yan bora kadai ake tursasawa kan batun cin hanci da rashawa. Sannan masu sharhi kan harkokin siyasa na kuma yiwa gwamnatin Obasanjo yar’amshin shatar turawan yamma da Amerika da bankin duniya ,domin manufofin da gwamnatin sa ke gudanawar daga su ya karbo.

Amma me yasa yan Nijeriya ke ganin laifin Shugaba Obasanjo musamman mutanen Arewa? Wasu suna zargin sa da cewa da gangan ya taimaka wajen ganin cewaq Arewa bata sami cigaba ba kamar mutanen kudancin Nijeriya musamman a fanning tattalin arzikin kasa inda yan kuddancin Nijeriya su suka fi cin gajiyar manufofin gwamnatin sa a bangaren sauye sauyen bankuna da sayar da kaddarorin gwamnati . Haka kuma wasu na zargin sa da baiwa mafi yawan mukaman gwamnati ga yan bangaren sa. Amma abin tambaya anan shine kudaden da gwamnatin tarayya ke baiwa jihohi da kananan hukumomi a matsayin kudin rabon kasa, shin gwamnoni da shugabannin kananan hukumomi sunyi ayyukan raya kasa ga jama’ar su? Sannan kuma yan Arewan da suka rike mukamai a gwamnatin sa sun kawo wa al’ummar da suke wakilta abubuwan more yaruwa?

Kowa ya tuna bara bai ji dadin bana ba, domin yan Nijeriya su sani koda sun manta cewa da Janar Ibrahim Babangida ya mika wa wanda ya lashe zaben 12 ga watan juni na shekarar 1993 da bamu sami kan mu a halin da muke ciki ba. Sannan hadin gwiwar su Janar Babangida da yan G-34 su suka tsaya kai da fata Obasanjo ya sake dawowa bias mulkin Nijeriya. Inda kuma a zaben 2003 bisa jagorancin Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar aka sake dankarawa yan Nijeriya Obasanjo.

Yakamata yan Nijeriya su yi karatun ta natsu su daina daura wa Shugaba Obasanjo duk laifufukan tabarbarewan al’amurra shi kadai! Ta bangaren sa ya lura da cewa masu kaiwa da komowa a matsayin shugabannin al’umma mutane ne masu tsananin son kan su, su kadai. Saboda haka ko wanne daga cikin su na da farashin sa da in aka taya zai sallama. Ya kuma fahimci cewa talakawan Nijeriya suma ta bangaren su , basu ma san inda aka sa gaba ba da rashin sanin hakkokin su .Wannan ko a bayyane yake kan yadda aka gudanar da zaben wannan shekarar inda duk da korafai korafai da ake maluman addini sune kan gaba wajen halasta sakamakon zaben.

Da masu cewa mulki ya komo Arewa ko kuma ya komo hannun Musulmi lokaci ne kawai zai tabbatar in da gaske suke yayin da kida ya canza.Domin wasu daga cikin su har zalamar su tafara fitowa fili bias mubaya’ar da suka yi wa Shugaba mai jiran gado Alhaji Umaru Musa Yar’adua .Yayin da hakar su ta kasa cimma ruwa muna sauraron me zasu fito su fadawa yan Nijeriya.

Shugaba Obasanjo dai tasa ta kare a bias jagorancin da yayi wa yan Nijeriya , tarihi a sannu zai bayyana matsayin sa kan yayi abin kirki ko akasin sa. Yan jari hujja da masu hannu da shuni ba shakka sun ci gajiyar mulkin Obasanjo , a yayin da talakawa musamman wadanda yan’uwan su suka rasa rayukan su a rigingimun kabilanci da addini ko kuma dubban talakawan da aka raba su da aiyukan su ko muhallin su da sana’ar su musamman a birnin tarayya Abuja zasu yi takaicin mulkin Obasanjo. Haka kuma tarihi zai bayyana irin gudumawar da Shugaba Obasanjo ya bayar ga bunkasar dimokaradiyya ko wanin sa . Da fatan in ya koma gonar sa ta Ota zai kyale sabon shugaban kasa ya gudanar da ayyukan mulkin sa ba tare da fuskantar katsalandar saba cikin harkokin mulkin sa.

Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com