Tuesday 29 July 2008

As the gap between politicians and masses gets wider.

Politics in Nigeria is a serious business a do or die affair as it is the shortest route to riches. With the amount of money given to politicians legally as salaries and allowances excluding the spoils of the office , the politicians have been placed in the legion of millionaires .There is no politician , from councillorship upward , that is not a millionaire!



As for the Nigerian masses , they are getting poorer and poorer by the day. Inflation , unemployment , job insecurity, underpayment and delay in payment of salaries have bugged down the poor masses and denied them the living they are supposed to enjoy in a nation blessed with abundant natural resources.



The gap between politicians and masses is getting wider by the day , even as teachers embark on a national strike to demand for increase of salaries and allowances which the government has refused to implement under flimsy excuses, politicians on the otherhand have cause to smile to their banks as their salaries and allowances have increased in millions.



Even as children of the masses roam the streets as hawkers , petty labourers and beggars as all public schools are closed due to teacher's strike, the children of politicians from Mr. President to Honourable Councillor are in their classrooms in expensive private schools. And if not, between Mr. President, his vice and ministers , leadership and members of the National Assembly , state governors and their commissioners who among them do his children attend public schools and is affected by the present teachers strike? If there is anyone among those listed above, i will willingly surrender myself for ten strokes of cane!



If the Nigerian politicians would have five increases in their salaries and allowances from 1999 to date, how many increases in salaries and allowances have the Nigerian workers got from 1999 to date?(with apology to those not fortunate to be working). Don't they also need increase in their salaries and allowances to curb the menace of inflation? How much is minium wage ? What was the price of bag of rice in 1999 and what is it today? Is miniunum wage enough to buy a bag of rice today? Excluding amount spent on other household items, rent, transport , medical bills, school fees , utility bills e.t.c ?



We are a nation of hypocrisy and deceit as we all know what is being paid to Nigerian workers as salaries and allowances cannot fulfill their basic neccessities of life. Are the politicians more Nigerians than the masses? Are the politicians our first class citizens? In the course of nation building are some more important than others?



If not of selfishness and greediness that have characterised the way of life of Nigerian politicians , why would'nt they use their offices to alleviate the sufferings of their people and live by setting examples. Benefits of the offices they occupied are numerous from free accomodation, transport, medicals, food ,utility and free of whatever you can think of to make life comfortable and easy. But due to their greed the very little the masses demand to assist in keeping them moving is being denied them. It is only masses' demands that meet shortage of funds and deficits. And if they insist on their rights they are threatened with retrechentment and downsizing.



Nigerian masses are philosophical and as such take life easy and simple. As far as the masses are concerned, if they can eat to their satisfaction , pay their house rents, have an atmosphere that is condusive to conduct their legitimate daily activities, being able to solve their family educational and medical needs, e.t.c, the politicians can go and do whatever they want with the nation's resources. But why are the politicians wicked and inhuman? Why should a single person steal billions he cannot use and dump them in foreign banks? The Nigerian politicians should know that tyranny and deceit will not last forever as the dumbfounded and oppressed will one day realise the difference between his left hand from the right.



Disenchantment, mistrust, loss of confidence and hatred are growing all over the country against politicians. Masses cannot comprehend what is being done with billions of dollars the country is earning due to daily increase in international oil price. When some countries among those benefitting from the oil windfall embarked on building five new cities and some using theirs to advance nuclear technology to produce energy , we , the masses here are still living in hunger and lack of basic necessities of life. Politicians should as a matter of urgency act to start implementation of policies that the masses can testify tht yes they have a caring , accomodative and listening goverment.



Politicians at the helm of affairs from Federal,State and Local goverments have all performed below expectation with huge amounts of monies being shared among them. No good roads , drinking water,education, medical facilities,electric ity e.t.c.. And they also cannot solve the issue of unemployment which has turned strong,energetic and it is turning able young men and women into beggars ,criminals,fraudter s,prostitutes and frustrated people. The issue of unemployment has even taken a new dimension as monies are being extorted from applicants and they can easily lose their lives in the course of seeking for employment.



Other Nigerians , like politicians need equal oppurtunities and actions in place of rhetorics , sincerity in place of deceit ,good governance and a free and fair election. It is quite unfortunate for our politicians to be unable or delibrately refuse to fulfill the promises they make to the electorate when seeking for political office. Present politicians have no excuse for not performing as the resources are there and more than enough to bring about changes in the lives of ordinary Nigerians.



For any nation to develop , it has to invest heavily in the educational sector . With this , I am appealing to President Umaru Musa Yar'adua if he is sincere in achieving his seven-point Agenda, among which education is prominient to , as a matter of urgency , live by example in removing his children from private schools and take them to public schools and order all his officials and party to do the same and satisfy teachers demands. Let's see if quality of education will not change immediately.



The earlier Nigerian politicians realise that the masses are watching them enjoying their lives of comfort, while they allow them to continue to live in darkness , insecurity and fear of uncertain future the better. They too ( masses) like politicians , want their dividends of democracy through good living atleast one percent out of ten of how politicians live.







Shehu Mustapha Chaji

shehuchaji@yahoo. com

Saturday 26 July 2008

Rayuwan yan siyasa da talakawa na kara tazara!

Irin makudan kudaden da ake samu a harkar siyasa a yau ya sanya siyasa kan gaba wajen harkar da tafi kawo kudi a yau a Najeriya. Manoma da yan kasuwa da ma’ikatan gwamnati a yau ko kusa basa samun kudin shiga kamar yan siyasa. Makudan kudaden da yan siyasa ke samu daga albashin su da alawus-alawus zuwa maikon dake tattare da kujerar da suke kai ya sanya su a sahun masu hannu da shuni. A yau babu dan siyasa daga Kansila zuwa sama da bai bawa miliyoyi baya ba !



Shi kuma talakan Najeriya a kullum sai kara talaucewa yake yi. Hauhawan farashin kayayyaki da rashin aikin yi da rashin tabbas kan aiki da sana’oi da kuma karancin albashi ya sanya talaka na rayuwa cikin matsi duk da dinbin arzikin kasa daga ma’adinai da kudin shiga da gwamnati ke samu a kullum.



Banbancin rayuwa tsakanin yan siyasa da talakawa na kara nisa a kullum. Duk da cewa Malaman makarantu sun shiga yajin aiki kan batun Karin albashi da gwamnati har yanzu taki sauraron su saboda wasu dalilai da hankali ba zai kama ba. Su kuma yan siyasa an kara masu albashi da alawus-alawus na miliyoyin nairori.



Ya’yan talakawa a yau nata garanramba da tallace-tallace da aikin leburanci da bara sakamakon yajin aikin malaman makaranta. Su kuma ya’yan yan siyasa daga Shugaban Kasa zuwa Kansila suna karatun su a makarantu masu zaman kansu masu tsada. Daga Shugaban kasa zuwa Mataimakin sa da ministocin da yan majalisar tarayya da shugabannin su da gwamnonin jihohi da kwamishinonin su , waye a cikin su da ya’yan sa ke zuwa makarantun gwamnati kuma wannan yajin aikin ya shafe su? In an sami daya cikin wadanda na lissafa a baya ya’yan sa na zuwa makarantun gwamnati , to a shirye nake ayi mani bulala guda goma.



In har yan siyasa zasu sami Karin albashi da alawus-alawus har sau biyar daga 1999 zuwa yau, su kuma talakawan kasa fa? Ko su basa bukatar Karin albashi ne? Nawa ne mafi karancin albashi? Kuma nawa ne kudin buhun shinkafa a yau? Sannan ga kudin cefane na yau da kullum da kudin haya da sufuri da asibiti da makaranta da wutan lantarki da ruwa da sauran su.



A yaushe zamu daina munafunci da yaudara a kasar mu? Kowa ya san cewa albashin da ake baiwa ma’aikata a Najeriya baya isar su biyan muhimman bukatun rayuwan yau da kullum. Su yan siyasa sun fi zama yan Najeriya ne kan talakawa? Sannan su yan siyasa wasu mutane ne na musamman? Wasu sun fi wasu muhimmanci ne a bada gudunmawar gina kasa?



In banda zalama da son kai irin na yan siyasar Najeriya me zai hana su yin amfani da mukaman su wajen aiwatar da ayyukan da zai rage ko kawo karshen wahaloli da kuncin rayuwa daya dabaibaye talakawan su da kuma bada kyakyawan misali? Romon dake tattare da mukaman da suke kai nada yawan gaske, inda suke more gidan kwana da motoci da kiwon lafiya da abinci da sutura da duk kayayyakin more rayuwa a kyauta. Amma saboda son kai dan bukatun da talakawa ke bukata dan tallafa masu a rayuwar yau da kullum an hana su. Bukatun talaka kadai ke gamuwa da rashin kudin da tsuke bakin aljihun gwamnati. In kuma suka dage kan neman biyan bukatun su sai ayi masu barazana da rage ko korar su daga aiki.



Talakawan Najeriya sun kasance masu hakuri da dogaro ga Allah wanda hakan ya sanya su basa daukan rayuwa da zafi. Buri da bukatar talaka bai wuce samun abinci sau uku a rana ba da samun halin biyan kudin haya da samun kyakyawan yanayin da zasu gudanar da harkokin neman halaliyar su na yau da kullum. Su kuma iya biyan kudin makarantan ya'yan su da magungunan da akan rubuta masu su saya a asibitoci da sauran su. In talaka zai iya biyan bukatun dake gaban sa , to yan siyasa suje suyi duk abinda suka gan dama da dukiyar kasa. Me yasa yan siyasa suka zama mugaye marasa tausayi da imani? Me zai sa mutum daya shi kadai ya saci biliyoyi da bazai iya amfani dasu ba ya kaisu bankunan kasashen waje ya boye? Yan siyasar Najeriya su kwan da sanin cewa zalunci da yaudara ba zai dore ba , saboda wata rana talaka da ake zalunta zai fahimci banbanci tsakanin hannun hagun sa da dama.



Rashin yarda da zargi da kiyayya nata yaduwa a ko'ina cikin kasar nan kan yan siyasa. Talakawa sun kasa fahimtar me ake da biliyoyin dalolin da kasar ke samu albarkacin hauhawan farashin man fetur a kasuwar duniya. Wasu kasashe cikin wadanda suke cin gajiyar hauhawan kudin man fetur har su kaddamar da gina sababbin birane guda biyar , yayin da wasu suke amfani da nasu wajen gina masana'antar nukiliya dan samar da makamashi. Mu kuma a nan talakawa na cigaba da rayuwa cikin yunwa da rashin abubuwan more rayuwa. Ya kama yan siyasa su gaggauta kaddamar da aiyuka da manufofin da talaka zai shedi cewa yana da shugabanin masu tausayi da sanin ya kamata.



Yan siyasar dake tafiyar da al'amurran mulki daga gwamnatin tarayya da jihohi zuwa kananan hukumomi duk sun gaza wajen aiwatar da ayyukan cigaba kwatan-kwacin makudan kudaden da suke rabawa a tsakanin su. Babu kyawawa da ingantattun hanyoyi da ruwan sha da ilimi da kiwon lafiya da wutan lantarki da sauran su. Kuma sun gaza warware matsalar rashin aikin yi da ya maida matasa majiya karfi almajirai da masu aikata laifuka da karuwai da kuncin rayuwa. Matsalar rashin aikin yi ya dauki sabon salo inda ake tatsan su kudade dama iya rasa rayukan su a wajen neman aiki.



Sauran yan Najeriya kamar yan siyasa na bukatar a basu damar su da hakkokin su da cika aiki maimakon dogon turanci da kyautata niyya maimakon yaudara da mulkin adalci da zabe na gaskiya. Abin takaici ne ace yan siyasa suki cika alkawarukkan da suka yiwa talakawa yayin neman kuri'ar su . Yan siyasa masu ci a yanzu basu da wata hujja na kasa yin aiyukan cigaba saboda makudan kudaden da suke samu a yanzu.



Duk kasar da take son taci gaba ya wajabta ta kashe kudade masu yawa wajen bunkasa harkan ilimi , da wannan nake kira ga Shugaban Kasa Alhaji Umaru Musa Yar'adua inda gaske yake kan aiwatar da kudirorin sa guda bakwai da ilimi ke da matukar muhimmanci daya gaggauta nuna misali ta fitar da ya'yan sa daga makarantu masu zaman kansu ya maida su na gwamnati, sannan ya umarci jami'an gwamnatin sa da yan jam'iar sa suma suyi hakan, kuma ya biya dukkan bukatun malaman makaranta . In yayi haka cikin lokaci kadan zamu gan canji me yawa a fannin ilimi.



Yan siyasan Najeriya in basu sani ba , to su sani talakawa na kallon yadda suke rayuwar su cikin jindadi da kwanciyar hankali yayin da su suke rayuwa cikin duhu da rashin tsaro da rashin sanin makomar su a rayuwa. Suma talakawa kamar yan siyasa na bukatar rayuwan jin dadi dan su more romon dimokaradiyya a kalla kashi daya cikin goma na irin jin dadin da yan siyasa ke fantamawa a cikin sa.



Hazawassalam



Shehu Mustapha Chaji

shehuchaji@yahoo.com
08038222575