Saturday 2 June 2007

SAMAR DA SABUWAR TASWIYAR HANYA GA MATAN HAUSAWA

Mata a kasar Hausa sun kasance cikin matan da akafi kulawa da su da kokarin ganin sun sami nagartattacen rayuwa kan sauran mata na wasu bangarorin Nijeriya.Hukumomi ma basu yi kasa a gwiwa ba wajen taimakawa mata a inda a jihohi da dama ana basu ilimi kyauta da kulawa ta musamman in suna da juna biyu a asibitoci har zuwa haihuwa. A wannan makalar in mukayi zancen matan Hausawa sun kunshi dukkan matan dake zaune a Arewacin Nijeriya.Kan batun ma wanene Bahaushe ? Zamu barshi dan tattaunawa a wani lokacin .
Duk da a bayyane za'a ga kamar rayuwar matan Hausawa na tafiya ba tare da wata matsala ba, amma a hakikanin gaskiya akwai matsaloli da dama da al'umma suka tsuke bakunan su akai , kuma ba'a wani kokari na ganin an samar da mafita ga wadannan matsalolin .Bisa fahimtar addini da al'ada , da ci da sha da muhalli da tufafarwa duk sun ta'allaka akan miji ,amma kuma sai mazaje da mataye suka yiwa wannan umarnin addini da kuma al'ada wata fahimta ta daban .Wato ta bangaren maza suka noke da fahimtar samun wata dama da zasu dankwafar da mata ta hanyar kin basu damar da zasu inganta rayuwar su su kuma bada nasu gudunmawar ga cigaban ungwanin su da garin su da kasa gabaki daya .Su kuma mata sai suka fake da samun wannan damar na samun bukatun rayuwa bisa tsarin addini da al'ada ,sai yasa suka zauna suka mike kafa basa wani kokari ko yunkurin ganin rayuwar su ta inganta.
Kafin wasu su yi mani kartattacen fahimta , ina magana ne akan yadda rayuwar mata a kasar Hausa ta ta'allaka kan maza ba tare da yin wani yunkurin da rayuwar matan zata inganta su tsaya da kafafun su ba. Duk da cewa matsalolin tattalin arziki a yau ya tilasta wasu mazajen da mata su samar wa kan su mafita ta hanyar koyon sana'oi da kasuwanci da karatu mai zurfi ta fannin addini da boko dan samun ayyukan yi.Amma har yanzu akwai mazan da burin su shine yiwa matan su na aure mulkin mallaka ta wajen toshe duk wata hanyar da zasu sami kudin shiga.Wasu mazan kuma koda sunyi wa budurwa ko matan da zasu aura alkawarin cigaba da makaranta ko aiki,da zaran sun aure su sai suyi mirsisi su ki cika alkawarin da suka dauka.
Saboda hana mata samun kudin shiga ta hanyar aikin yi ko kasuwanci ko sana'a shike zafafa kishi yayin da mazajen su zasu kara aure domin suna ganin duk abinda mijin nasu ya mallaka wata cima zaune zata zo a raba da ita.Haka kuma so dayawa in mijin talaka ne wanda bai mallaki abin duniya ba ,da zarar ya mutu ko wata lalurar rashin lafiya ya sami mijin sai iyalen su shiga halin kakani kani. Ta kan kai da an bar matan da ya'ya, ya rage gare ta tasan yadda zata yi dasu.
Wai ma shin mun taba tambayar kawunan mu me yasa matan Hausawa ke daukan maganan gado da muhimmanci?Sannan kuma me kesa mai mata fiye da guda matan nasa zasu yi ta gasar haihuwa?Shin me ke kawo takun saka tsakanin matan marigayi da yan'uwan sa wajen rabon gado? Kuma me ke yawan kawo rabon gado a kotuna tsabanin shekarun baya da ake rabawa a gida?
Tun ranar gini tun ranar zane ,mafi yawan maza in suka je neman aure zancen da suka fi yiwa mata shine na basu aljannar duniya wanda ke jawo wasu yan'matan ma in makaranta ko aiki suke sai su daina domin kakar su ta yanke saka.Zai fi kyau tun ana neman auren a rika karfafa wa mata gwiwa domin su fuskanci rayuwa ,su kasance suna da manufa da burin da suke so su cimma a rayuwa.So dayawa irin wannan baiwar kan bayyana ga wasu matan yayin da mutuwa ta raba su da mazajen su ko rabuwan auren.Da dama sun shahara ta fannoni da dama da suka zabar wa kan su.
Matan Hausawa na bukatar sabon tsarin rayuwa da zasu taimakawa kan su da mazajen su da ya'yan su da iyayen su da yan'uwan su.Suna bukatar tallafi da karfafa gwiwa kan abinda suka zabar wa kan su a rayuwa.In sana'a take sha'awa ,to a tallafa mata wajen koyon sana'ar da kuma girmama su in akazo harkar cinikayya . Sannan in makaranta take sha'awa to a tallafa mata da taimaka mata har ta cimma wannan burin nata . Haka kuma in aiki zata yi a taimake ta dayi mata kyayawan zato.Ta wannan hanyar lallai mata zasu bada babban gudunmawa ga bunkasar tattalin arzikin kasa.
A zamanin nan da muke ciki da mafi yawan yaran da ake haihuwa mata ne ,akwai bukatar dora su bisa tafarkin da zasu zama masu dogaro da kan su saboda in suka sami kan su a halin mutuwan iyayen su ko mazan su na aure ,ko in auren su ya mutu ko kuma rashin samun mijin aure da wuri , ba zasu kasance cikin wani mumunan hali ba,su kasance suna masu iya dogaro da kan su dama taimakawa wasu.Kuma a wannan zamanin na jari hujja da gwamnati ta janye kusan dukkan tallafi kan abubuwan more rayuwa,magidanta da dama na shan bakar wahala wajen baiwa iyalen su abubuwan jin dadin rayuwa.Shin ba abu mai kyau bane iyalen sa suma su bada nasu gudunmawa ga tafiyar da gida?
Domin a zamanin da muke ciki a yanzu in magidanci na bukatar ya'yan sa su sami nagartattcen ilimi sai ya kai su makarantu masu zaman kan su .Haka ma batun kiwon lafiya da sauran al'amurran tafi da rayuwa na yau da kullum. Ga halin rasa aiki ko sana'a da dubban magidanta suka sami kan su bisa sauye sauye a manufofin gwamnati ,shi ke nan in maigida ya sami kansa cikin tsaka mai wuya sai iyalen sa gaba daya su tagayyara?A kullum muna cin karo da gungun mata da ya'yan su masu tsaida mutane a kan hanya suna neman taimako ko in ce bara,da dubban kananan yara (musamman mata )da ake turo su daga kauyuka domin a'ikatau a gidaje a birane.
Sannan wani babban matsalar da ake fama da ita da kusan kowa ya tsuke bakin sa shine na matsalar yawan Zaurawa .Kusan yadda ake yawan aure ,haka ake yawan sakin matan ,ko kuma mazajen su gudu su bar matan! Me ke kawo yawan sakin mata a yanzu?Koma menene dalilan akwai bukatar samin bakin warware wannan matsalar na yawaitan Zaurawa.
Kungiyoyin mata da kungiyoyin mutunta hakkin yan'adam da matan shugabanni a kowane mataki bisa jagorancin Shugabanin addini ya kamata suyi kokarin ganin ana martaba mata tare da bi masu hakkin su yayin da mazajen su zasu sake su .A wannan lokacin na tsarin dimokaradiyya akwai bukatar neman majalisun dokoki daga jiha har tarayya su yi dokokin da dole in magidanci zai saki matar sa sai a kotu da biyan ta wasu makudan kudade da zai ishe ta tafi da rayuwar ta har ta sake aure. Mafi yawan masu sakin matan su nada ketar ganin matan su tagayyara su kuma rasa tudun dafawa .Haka kuma sau dayawa akan sha wahala da mata ana zaman aure ,amma da zarar walwala tazo sai mazajen su, su hura masu wutar kiyayya har sai an rabu,kiri kiri suna ji suna gani dadi yazo za'a ci babu su. Sannan ga maza marasa tausayi da suke sakin matan su in wata laluran rashin lafiya ta same su dan kawai kada su kashe kudin su wajen neman magani.Wasu mazan kuma dan hannun su da shuni sai su auri mata su sake su in suka cimma burin su !
Lokaci yayi da matan Hausawa zasu hada kafada da sauran matan kasashen da suka cigaba musamman na kasashen Musulmi inda suke da dama kamar kowa ta wajen samun ilimi mai zurfi da damawa asha dasu a harkokin kasuwanci da kimiyya da siyasa.Amma wannan damar ba zata samu ba sai sun yinkuro da kan su domin ganin cewa ana basu damar da addinin su ya basu ,tare da juya baya ga duk wata al'ada da zai tauye cigaban su a rayuwar zamanin mu na yau domin su bada tasu gudunmawar ga bunkasar tattalin arziki da cigaban Arewa da Nijeriya.

Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com
http://shehuchaji.blogspot.com/

1 comment:

  1. Loved your site, Lee! Thanks for sharing Kami menyediakan berbagai macam obat seperti Obat kondiloma , Kencing Nanah , Wasir , Sipilis , Herpes , Diabetes

    ReplyDelete