Thursday 29 May 2008

Shekara daya bisa mulki: Shugaba Yar’adua a kan mizani

A kwana a tashi ranar 29 ga watan Mayu na wannan shekarar Shugaba Umaru Musa Yar’adua ya cika shekara daya bisa kujerar mulkin Nigeriya. Zaben daya dora shi bisa mulki ya sami suka daga kungiyoyin sa’ido na cikin gida da kasashen waje da jam’iyyun adawa saboda zargin an tafka magudi, wanda ya kaiga shigar da karairaki a gaban kotuna , inda a halin yanzu ana jiran kotun koli ta halasta ko kuma ta soke zaben nasa.
Ya kama aiki a wani yanayi na neman goyon bayan jama’ar kasa , ga kuma yajin aiki na gama gari da kungiyar kwadago ta kasa ta kira saboda neman ya warware wasu manufofin gwamnatin tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo na sayar da matatan man fetur na Kaduna da Fatakwal da Karin kudin man fetur da haraji. Bayan amsa kiran yan Nijeriya ta hanyar biyan bukatun kungiyar kwadago ta kasa ta data nema , ya dauki alkawarin inganta rayuwan yan Nijeriya ta hanyar aiwatar da kudirori guda bakwai.
Ginshikin mulkin Shugaba Yar’adua kamar yadda ya sha fada zai kafu ne bisa kudirori guda bakwai . Kudirorin sune bunkasa wutar lantarki da samar da tsaro da samun yawaitar arziki da samar da ingantattacen ilimi da kawo sauye-sauye a dokar filaye da kyakyawan tsarin sufuri da warware matsalar yakin Neja Dalta . Amma abin lura da tambaya shine ko Shugaba Yar’adua ya kama hanyar cimma burin sa na kudirorin guda bakwai ? Kuma cikin kudirorin guda bakwai wannene ya warware matsalar ? Sannan shin yana kan hanyar aiwatar da kudirorin guda bakwai? Kuma shin talakawan Nijeriya zasu shedi banbanci a gudanar da yanayin mulkin sa dana tsohon shugaban kasa Obasanjo?
A zancen gaskiya har yanzu yan Nijeriya basu fara amfana da kudirorin bakwai na shugaba Yar’adua ba. In mun dauki wutar lantarki, a kullum lamarin sai kara tabarbarewa yake tayi inda yanzu wutar da ake samu ya gaza awa biyar a rana. Kuma har yanzu yan Nijeriya na sa’ido domin ganin ya saka dokar tabaci a kan wutar lantarki kamar yadda yayi alkawari. Sannan in muka dauki fannin samar da tsaro har yanzu yan kasa na fuskantar barazanar masu aikata muggan laifuka. Kazalika matsalar yankin Neja Dalta na nan inda tsagerun matasa masu dauke da makamai nata cigaba da kawo cikas a harkokin hakan man fetur inda ake hako kasa da ganga miliyan 2 a rana maimakon ganga miliyan 2.4. Fatara da talauci da rashin aikin yi da kuma hauhawan farashin kayayyaki ya tasa talakawa a gaba duk da makudan kudade da gwamnatin ke samu .
Tun hawan sa bisa mulki masana harkokin siyasa ke zargin cewa Shugaba Yar’adua na mulki da sanyin jiki wanda ya janyo harkokin gudanar da mulkin kasa keta tafiyar hawainiya. Suna kuma ganin cewa har yanzu kamar ya kasa gano kan zaren matsalolin dake damun kasar , ga kuma ayi gaba ayi baya kan manufofin gwamnatin sa. Akwai masu ganin cewa mulkin sa cigaban mulkin tsohon shugaban kasa ne Cif Olusegun Obasanjo . Wannan shi yasa ma wasu suke ganin cewa babu wani cigaba da aka samu a shekara daya da yayi yana mulki.
Amma wani abin lura game da gwamnatin Shugaba Umaru Yar’adua shine na kokarin bin doka da oda, inda yake ta kokarin ganin cewa ana bin dokokin tsarin mulkin kasa da bin umarnin kotu sabanin gwamnatin da ta shude. A shekara daya na mulkin sa, Shugaba Yar’adua na bin hukuncin kotuna da suka yanke musamman gwamnonin jam’iyyar sa da kotuna suka soke zaben su, shima kansa yayi alkawarin cewa in kotun koli ta soke zaben sa zai sauka a take ya kuma mika mulki ga wanda kotu tace a mika masa mulki. Koda yake yan adawa na zargin cewa ta bayan gida ana tsoma baki a harkokin shari’a inda suke zargin sa hannun Uwargidan sa Hajiya Turai Yar’adua da hannu a shari’ar data tabbatar da kujerar gwamnan jihar Kebbi Alhaji Sa’idu Usman Nasamu Dakin Gari domin surikin sune. Duk da haka babu zargi kai tsaye na cewa shi Shugaba Yar’adua da kansa ne ya tsoma baki a batun shari’ar.
Kuma tun hawan sa mulki babu zargin cewa yana sama da fadi da dukiyar al’umma kamar a gwamnatocin baya. Sannan ba’a zargin sa da yada cin hanci da rashawa ko kuma bada cin hanci ga yan majalisun kasa dan cimma manufofin sa. Haka kuma ba’a zargin sa da dakile ko kuma kawo cikas ga aiyukan majalisun tarrayya da kawo cikas a aiyukan sashin shari’a.
Yan Nijeriya nada bukatar ganin cewa gwamnatin Shugaba Yar’adua na gudanar da aiyuka na zahiri da zai inganta rayuwar su, kamar samar masu da aiyukan yi da gaggauta kawo karshen matsalar wutan lantarki da rashin sa ke kawo cibaya ga bunkasar tattalin arzikin su da bunkasa aikin gona ko kuma a takaice ya aiwatar da kudirorin sa guda bakwai kamar yadda yayi masu alkawari. Sannan kuma a aikace ya tabbatar da ana zabe na gaskiya kamar yadda yayi alkawari domin baiwa yan kasa kwarin gwiwa kan cewa lallai Nijeriya na bin tsarin dimokaradiya.
Har yanzu mafi yawan yan Nijeriya nayi wa Shugaba Umaru Yar’adua kyakkyawan zato na cewa kila abinda kesa yake jan kafa wajen gudanar da mulkin sa shine na karar dake gaban kotun koli . Ya wajaba a gare shi ya kasance tare da yan Nijeriya ba wai wani ko wasu mutane ba saboda sun tsaya masa ya zama shugaban kasan Nijeriya ba. Lokaci dai baya jira a inda a yanzu har ya shafe shekara daya yana mulki.
Inda za’a gudanar da kuri’ar jin ra’ayin mutanen Nijeriya da mafi yawan su zasu ce su har yanzu basu gani a kasa ba. Rayuwar su babu banbanci da shekaru takwas da Obasanjo yayi yana mulki, kuma sun fara fidda rai kan cewa mulkin Shugaba Yar’adua zai kawo canji a rayuwar su. A watanni masu zuwa yan Nijeriya zasu iya tabbatar da cewa zasu sami canjin da suke tsammani ko kuma cigaba da rayuwa kamar yanda suka shafe shekaru takwas na mulkin Obasanjo cikin matsi da kuncin rayuwa duk da arzikin da kasar ke samu albarkacin hauhawan farashin man fetur a kasuwan duniya.

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Tuesday 27 May 2008

OH YEAH NIGERIAN MASSES

Hope as the motivating factor that keeps the Nigerian masses going as usual , today is giving them the courage to withstand the present hardship which has to do with exorbitant prices of food stuff and materials needed for their daily use. Inflation is on the move like wild bush fire consuming and destroying whatever stands on it's way. Worse still, income of Nigerians is not increasing in propotion to the inflation rate, if they are even lucky to have something doing as a means of livinghood.

Insecurity is on the rise.With all security operations, this and that going on in most states of the country . Armed robbery, assasination and thuggery are on the rise and the situation is so bad that in some parts of the country, where in previous years, armed robbery was alien especially on the roads, has now become order of the day , as armed robbery could occur at any time of the day.

Health, which is one of the responsibilities of goverment has been left under funded. If the Nigerian mass is unfortunate to be sick , he/she is in deep trouble as there is a berlin wall of naira between him/her and the hospital. The cheap source of medication to the common man is the traditional concoctions which he can afford. And if the sickness is so bad that there is need for an operation or expensive drugs, it is either- if they have the connection- to seek for public assistance through the media or lie down at home and wait for death. Due to goverment attitude toward provision of basic health amenities which is not forth-coming , it has led to providing booming trade to private hospitals and traditional medicine sellers.

Qualitative education is beyond the reach of Nigerian masses. Public schools now cannot compete with private schools in providing qualitative education as even children of our leaders wards are not attending the schools. Education provides many oppurtunities in life which is even the reason today that children of the poor and downtrodden are able to have the good things of life and even become leaders in their societies. The Elites of today have used their positions to deny the children of the masses the oppurtunity they need to obtain education through implementation of anti-people policies. They have also succeeded in segragating our societies through provision of different schools for the poor and rich from primary schools to universities as their ways will never cross in seeking for knowledge and the quality of jobs after school.

Unemployment also remains one of the problems affecting the Nigerian masses. The trade they are into is congested due to the number of those involved in the trade such as barbers, okada riders, petty trading, selling of recharde cards, labourers e.t.c and they cannot even satisfy their basic needs of day to day living. Due to non availability of power supply which has led to closure of many industries, Nigerian masses have been sent into labour market. Even those employed presently in public and private sector are not comfortable as they can lose their jobs any time in the name of reforms.

The Nigerian masses' votes no longer have any value as those they elect are different from those declared as winners.During election period political , traditional and religious leaders summon the masses to go out enmass to cast their votes, which sermon they oblige to as masses do come out enmass , men and women, to cast their votes. Unfortunately the elections are often rigged and those leaders will come back and lecture them that power belongs to the Almighty! Due to the behaviour of votes stealers and manipulators the masses are now having a second though on future elections as they would not want their times to be wasted.

For a very long time to come Nigerian masses will be taken for a ride as far as they cannot distinquish between justice , tribalism and sectionalism. The elites use the tricks of power shift and rotation to continue to confuse the masses as they mostly have one common agenda of protecting their political class and their intrests.

If Nigerians will allow themselves to be deceived with the issue of return of power to their region or those they share the same faith affiliation with, even if they came through the back door closing their eyes to their ability and capability to lead the nation , it will take a long time for us to have dedicated leaders.

The Nigerian constitution is clear on what are the rights of the Nigerian people , the Nigerian masses should not allow their rights to be infringed on and be turned into second class citizens in their own country. The Nigerian masses should never believe in the propaganda spread that things will never be alright in their country. That there will never be a free and fair election, that corruption is in their blood, that those in authority cannot be quetioned e.t.c. The masses should believe that things will one day be better in their country and they should collectively strive toward this attainment.

It is well known that the Nigerian problem lies in lack of dedicated and good leadership. Any day they are lucky to have a leadership with people's intrest and concern at heart, a focussed leader that attains power legitimately, fearless and not a cohort or errand , surely the country will be on the path of progress and greatness.

Tricks used by the political elites should be understand by the masses as they (the masses) are to be discouraged from democratic process so that they can have a free hand to do whatever they want. The masses should come out enmass during future elections and try to make sure that their votes are counted as they are as it happenned in some states during previous elections . If they refuse to come out to cast their votes in future elections, they should be ready to continue to live under civilian dictatorship in the guise of democratic governance.

It is a duty on all Nigerians to ensure that we have good governance. If they allow themselves to be bought with as little as two hundred naira and some toilet soaps, they are not being fair to their contry. All over the world countries are fast developing especially those with petroleum resources, where food stuffs of the common masses are rice, milk and chicken. But in our own Nigeria with all the billions of dollars gotten from petroleum products , food stuffs like gari, amala and tuwo are not guarentteed three times a day. our politicians lack development ideas to lead our country to greatness, as building of water wells , drainages and distribution of motocycles are achievements they can boast of while in office.

Oh yeah the Nigerian masses when shall you strive for your nation to attain the greatness it deserves in the comity of nations ?


Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Thursday 8 May 2008

Shekaru 60 na mulkin PDP: Zancen Ogulafor da kanshin gaskiya

Yerima Vincent Ogulafor , Shugaban jam’iyyar PDP na kasa a kwanananan ya sanar da yan Nijeriya cewa jam’iyyar sa zata mulki Nijeriya na tsawon shekaru 60. Zancen na Ogulafor ya janyo masa suka daga masoya bin tsarin dimokaradiyya na hakika, sannan cikin zantuttukan nasa ya nemi da Nijeriya ta kasance kasa mai bin tafarkin jam’iyya guda daya rak.
Jam’iyyar PDP ta saba da aikata wasu abubuwa daya sabawa tsarin dimokaradiyya. Kuma abin abin mamaki shine yanda suke son abubuwa su kasance haka nan yake kasancewa ko ana so ko ba’aso. Kafin tsohon Shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya kamala wa’adin sa na farko, tsohon hambareren shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar ta PDP Cif Tony Anenih yayi shelar cewa babu gurbi ga wani sabanin Obasanjo dake da niyyar zama a fadan mulkin kasa ta “Aso Rock” . Haka zancen ya kasance inda PDP suka tabbatar wa yan Nijeriya cewa babu gurbi a fadar Aso Rock , kuma abubuwan da suka faru bayan haka a yau ya zama tarihi.
Obasanjo da kansa shima a lokacin yakin neman zaben 2007 ya fadi cewa zaben na 2007 zabe ne na “ko a mutu ko ayi rai”, kuma tabbas sun tabbatar wa yan Nijeriya cewa zaben na 2007 na a mutu ko ayi rai ne domin har yanzu kasar da yan kasar basu gama farfadowa da irin mamayan da PDP tayi masu ba. Koda kotunan zabe sun soke wasu zabubbukan na jam’iyyar PDP , jam’iyyar ta bayyana niyyar ta na ganin cewa yan takarar ta da aka soke zaben su, su zata sake tsayarwa dan su koma kan mukaman su, jam’iyyar ta tabbatar da haka a zaben da aka sake a jihohin Kogi da Adamawa.
Wai shin me yasa jam’iyyar PDP ke samun yadda take so ne a kullum? Shin korafe-korafen da yan Nijeriya keyi kan jam’iyyar PDP da yanda ta keta hurumin zabe a zaben 2007 da gaske suke yin ta? Sannan yan Nijeriya suna goyon bayan jam’iyyar PDP ne da yasa ita kadai ce jam’iyyar da ta wasu a ko’ina cikin kasa? Shin gwamnatin PDP ta aiwatar da ayyukan cigaban kasa ne a tsawon shekaru 9 da har yasa yan Nijeriya ke son baiwa jam’iyyar goyon bayan har na shekaru 51 masu zuwa? Lallai yanda al’amurra ke tafiya da kyar in PDP basu yi shekaru 60 suna mulki ba, sai dai in bisa hanya yan Nijeriya sun farga da sanin hakkin su na hakika a tsarin demokaradiyya da kuma samun dammar kidaya kuri’oin su kamar yadda suke.
A yanzu haka jam’iyyar ta shafe shekaru 8 tana mulki. A yanzu kuma Shugaba Umaru Musa Yar’adua ya shafe shekara 1 cikin 4 na mulkin sa a zangon farko (mance da zancen shari’ar dake gaban kotun koli), yayin da zai kamala wa’adin sa na farko jam’iyyar PDP zata ta shafe shekaru 12 tana mulki. Kuma da alamun cewa Shugaba Yar’adua zai ci moriyar gyaran kudin mulkin kasar nan inda kila ayi zancen maida wa’adin mulki zuwa zango guda na tsawon shekaru biyar ko shida , sannan dokar ta fara aiki a shekarar 2011, in ka lissafa shekaru biyar ko shida PDP zata shafe shekaru 17 ko 18 tana mulki.
Kamar yadda aka saba in Shugaba Yar’adua ya kamala wa’adin sa na zangon farko sau biyu(?) sai mulki ya koma kudu kamar yadda Obasanjo ya aiwatar a aikace. Mataimakin Shugaban kasa , Jonathan Goodluck na jira inda shima inda rabon sa ya shafe shekaru 8 a wa’adin zango biyu ko shekaru 5 ko 6 a wa’adi guda a inda a shekarar 20….., PDP zata shafe shekaru kusan 30 ko fiye tana mulki.
Zancen da Ogulafor yayi na samun tsarin jam’iyya daya rak na bisa hanya saboda jam’iyyun da ake kira na adawa a yau sun zama masu fuska biyu kuma yan amshin shatar jam’iyyar PDP . Babbar jam’iyyar adawa ta ANPP a yau ta sami kanta a halin tsaka mai wuya inda ya’yan jam’iyyar nata tururuwan fita daga jam’iyyar zuwa jam’iyyar PDP, wasu kuma sun raba kafa suna makale a kan Katanga kamar gizago. Gwamna Ali Modu Sheriff na jihar Barno , ya bayyanawa Shugaba Yar’adua gaba da gaba cewa in har kotu ta soke zaben sa , to shi da magoya bayan sa zasu yiwa Yar’adua yakin neman zabe . Shi kuma tsohon gwamnan jihar Zamfara Sanata Ahmed Sani, Yeriman Bakura, cewa yayi yana da burin ya mulki Nijeriya , kuma ta shiga jam’iyyar PDP kawai ne zai iya cimma burin sa. Shi kuma Gwamna Isa Yuguda na jihar Bauchi nata kaiwa da komowa domin ganin ya auri diyar Shugaba Yar’adua, in ya cimma burin sa to da wuya ya kasance cikin yan adawa suna adawa da sirikin sa.
Jihohin Kano da Zamfara da suka kasance a sashin Arewa maso yamma shiyyar da Shugaba Yar’adua ya fito , tabbas PDP zata so ta kafa gwamnatoci a jihohin . Ta bangaren jihar Zamfara , tuni Yerima yayi alkawarin komawa jam’iyyar PDP dashi da jama’ar sa . Amma a bangaren Jihar Kano sai da yan dabaru, kuma tuni abubuwa na nuni ga irin rawar da Gwamna Ibrahim Shekarau zai so ya taka bayan ya bar mulki a shekarar 2011. Da alamu Gwamna Shekarau zai so ya taka rawa a siyasar tsakiya kamar yanda takwarorin sa a da gwamnoni sannan a yanzu sanatoci wato Saminu Turaki da Adamu Aliero . Magoya bayan Shekarau tuni suka mika amincewar su da goyon bayan su game da yadda Yar’adua ke tafiyar da kasar nan bisa ayyukan cigaba , sannan labarai nata yawo kan cewa Shekarau da Yar’adua “abokai ne na makaranta” a jami’ar Ahmadu Bello ta Zaria, kuma matan su aminan juna ne, shi yasa ma matar Shekarau tana cikin sahun farko da suka fara zuwa yiwa Yar’adua murna bayan hukumar zabe tace shine ya lashe zaben 2007.
Ta bagaren jam’iyyar A.C tuni ta dare gida biyu da masu son shiga gwamnatin hadin kan kasa da masu adawa. Kuma tuni gaggan jam’iyyar keta ficewa suna komawa jam’iyyar PDP kamar su Alhaji Abubakar Rimi da Alhaji Ghali Umar Na’abba.
Inda gaske yan Nijeriya suke na son bin tsarin dimokaradiyya to da jan aiki a gaban su . A matakin farko yan Nijeriya na bukatar zabe na gaskiya a inda za’a kidaya kuri’oin su kamar yadda suke. Tsarin dimokaradiyya ya ginu ne bisa wakilci na hakika da shugabanci na gari. Magudi da murdiyar zabe da dankara wa jama’a wanda bashi suka zaba ba yayi nesa da hakikanin tsarin dimokaradiyya na gaskiya. In za’a gudanar da zabe na gaskiya yan Nijeriya basu damu ba in jam’iyyar ta PDP zata shafe shekaru 1,000 tana mulki ba wai ma shekaru 60 da Ogulafor ke fadin zasu yi ba.
Yan Nijeriya na bukatar jam’iyyun adawa na gaskiya wadanda zasu jajirce wajen adawa na gaskiya , ba wai jam’iyyun adawa dake amfani da dammar su domin cinikayya da jam’iyya mai mulki ba dan biyan bukatun kansu ba
Hazawassalam
Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

KALUBALEN DAKE GABAN HUKUMAR FRSC

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (Federal Road Safety Commission)a bana ta cika shekaru ashirin da kafuwa . an dai kafa hukumar FRSC a lokacin mulkin Janar Ibrahim Babangida , dan ta sa ido kan tabbatar da bin dokokin hanya a kan kanana da manyan hanyoyin mu da baiwa hukumomi shawarwari kan halin da hanyoyin suke ciki , kuma inda bukatar gyara, su sanar a gyara. Suna kuma wayar da kan direbobi da sauran jama’a kan alfarnun bin dokokin hanya. Hukumar ta FRSC tayi rawar gani duk da matsalolin da take fuskanta na kunen kashi daga direbobi da kuma kasa aiwatar da shawarwarin da take bayarwa ga hukumomi kan yanayin da hanyoyi kasar ke ciki.
Kasantuwar hadurra na abubuwan hawa na kan gaba cikin jerin abubuwan dake kashe bil adama , inda itace ta tara a jerin annobar dake shekawa da mutane lahira , inda take sanadiyar mutuwan mutane a kalla miliyan daya da dubu dari biyu a shekara a kasashen duniya tare da kusan mutane miliyan hamsin dake samun raunuka.Kuma masana a fegen na ganin cewa in ba’a dauki mataki ba nan da shekarar 2020 hadurra na iya sanadiyar zama annoba ta uku da zata rika hallaka bil adama a duniya.
Matsalar hadurran abubuwan hawa ta sanya a yau da kyar ka sami wani dan Nijeriya da wani nasa bai taba gamuwa da hatsari ba wala ya rasa ransa ko ya sami rauni ko kuma ya tsallake rijiya da baya ba. Amma me yasa har yanzu matsalar dada karuwa yake duk da kokarin da hukumar FRSC keyi? Duk da cewa hanyoyin mu a yau basu da cikaken inganci, bai isa ace rashin kyawun hanyoyin kawai ke janyo yawan hadurra ba. Akwai matsaloli kamar tukin ganganci da gudu fiye da kima da kazamin lodi dake sa karuwan hadurra a kan hanyoyin mu. Sannan uwa uba sakacin hukumomi wajen ganin cewa ana bin dokokin hanya kamar yadda ya kamata.
Shin zamu cigaba ne da zuba ido karfen nasara nata kashe mana mutane saboda sakaci da rashin kula? Zamu cigaba da zuba ido ne wasu yan kunan bakin wake dan suna rike da sitari suna jefa rayukan mu cikin hatsari ? Kuma a yaushe zamu daina yarda wasu suna fakewa da kaddara bayan sun cuche mu dan rashin kula da ganganci ?
Mafi hatsari cikin mutanen dake zirga-zirga bisa hanyoyin mu sune direbobin manyan motoci daga tirela zuwa tifofi da direbobin motocin haya daga bas zuwa direbobin kananan motoci da yan achaba. A kullum kabi manyan hanyoyi sai ka tarar da hatsari wanda ke sanadiyar mutuwan jama’a . A yau in tafiya ta kama ka , to kana kan siradin mutuwa saboda halin masu tuki a kan hanyoyin mu.
Daya daga cikin sakacin hukumar FRSC itace na kasa aiwatar da dokokin hanya kamar yadda ya kamata. Wai shin ina jami’an hukumar ta FRSC suke inda kusan dukkan motocin haya dake zirga-zirga a cikin gari da masu dogon tafiya sun maida mugun lodi ko overload kamar haka dama can ya kamata a rika lodi. Duk motocin haya a yau daga bas-bas zuwa kananan motoci suna loda mutane kamar dabbobi a inda zaka tarar da karamar mota daya kamata mutane uku su zauna a baya za’a loda mutum hudu ko biyar, sannan a gaba daya kamata direba da mutum daya zasu zauna sai ka tarar an loda mutum biyu ko uku bayan shi direban !Sannan har a cikin boot suke loda fasinjoji. Balle yan bas da zasu loda mutane har kan inji , ga kaya an lafta a baya da kan motar . Manyan motoci kam kamar su Roka abun ba’a cewa komai domin ga kaya an loda har can koli sannan ga mutane da dabbobi a can koli bisa kaya.
In harda gaske hukumar FRSC keyi na da’awar suna ganin ana bin dokokin hanya to ya zama tilas , ba sani ba sabo su rika tabbatar da cewa ana bin dokokin hanya. Sannan su tabbatar da cewa duk wanda ya karya dokan hanya to lallai ya fuskanci hukunci mai tsanani. Kuma su rika bincike kan musabbabin hatsari, sannan in aka sami direba da laifin tukin ganganci ko kazamin gudu ko sakaci da sauran su to su tabbatar da cewa doka tayi aiki a kansa da kuma soke lasisin tukin sa na har abada. Inda dokokin su keda nakasu sai su nemi gyaran fuska ga dokokin dan ya basu dammar yin aikin su kamar yadda ya kamata.
Sannan al’umma nada rawa na musamman da zasu taka wajen ganin cewa an sami raguwar hadurra a hanyoyin mu , musamman Malaman addini wajen fayyace wa mabiya bin hakkin haddi . Duk yayin da aka sami wani yayi tukin ganganci ko sakacin daya kai ga rasa rayuwa ko rayuka sai kaji ance wai an yafe! Lallai a wayar da kan jama’a kan muhimmancin bin haddi wato su bi kadin hakkin su. Sannan su daina tsuke bakunan su yayin da dan kunan bakin waken kan sitari zai kaisu ga halaka suna ji suna gani , da kai koken su ga hukumomi kan mai wannan mugun hali.
Hukumar FRSC nada jan aiki a kansu na kare rayuwa da dukiyoyin yan kasa daga hannun mugayen mutane dake fakewa da sitari su hallaka yan kasa. Suna kuma da bukatar tallafi kamar yanda sauran hukumomin tsaro ke samu daga gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da kamfanoni masu zaman kansu da sauran al’umma . Dukkan yan kasa ya kamata su tallafa wa hukumar FRSC domin ganin cewa an sami saukin samun marayu da masu takaba da nakasassu saboda kunnen kashi da mugun hali na wasu marasa tunani da rashin imani da rashin kan gado dan kawai suna tuki a kan hanyoyin mu.

Haza Wassalam
Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com