Sunday 30 September 2007

TUNAWA DA RANAR KUDUS: RANAR JADDADA GOYON BAYA GA PALASTINAWA

A watan Yuli na shekarar 1979 marigayi Imamu Ruhullah al-Khomeini(r.a)ya bada fatawa ga al'ummar Musulmin duniya da masoya 'yanci da adalci na cewa kowace ranar Jumma'a ta karshen watan Ramalana ta kasance ranar Kudus. Kuma wannan fatawar ita ta canza al-kiblar gwagwarmayar Kudus da Palastinawa daga gwagwarmayar yan kasanci da Larabawa zuwa wani al'amari da ya hau kan al'ummar Musulmin duniya.

Menene Ranar Kudus? Kudus ta kasance Palastinu ga al'ummar Musulmi,ga su kuma Yahudawa ta kasance kasar Isra'ila. A kasar Kudus Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas yake inda ya kasance al-Kibla ta farko ga Musulmi ,kuma Masallaci na uku mafi daraja bayan Ka'aba mai girma da Masallacin Manzo Muhammad(saw)dake garin Madinatun Munauwara.

Ranar Kudus ta kasance rana ta hadin kai a tsakanin Musulmin duniya domin tunkarar matsalar Kudus da ta kasance abunda ya shafi dukkan Musulmi,kuma ranar Kudus ta kasance ranar da Musulmin duniya zasu isar da sako da murya guda domin al'ummar duniya ta sani ko a sake tunatar da ita irin zaluncin da danniya da kama karya da cin mutumcin da Yahudawan kasar mamaya ta Isra'ila kewa al'ummar Palastinawa dama Musulmi musamman kasashen Musulmin dake makotaka da Isra'ila.Ranar Kudus ta kuma kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tattauna tare da nemo mafita game da halin da al'ummar Palastinu suka sami kan su da tono da bankado irin makirce-makircen da kasar mamaya ta Isra'ila kewa Palastinawa da al'ummar Musulmi a ko'ina cikin duniya.

Shekarun bayan yakin duniya na biyu zasu kasance a bin tunawa da jimami ba wai ga al'ummar Palastinu da Musulmi kadai ba ,a'a harma da masoya 'yanci da adalci da walwala a ko'ina cikin duniya saboda mamayar zalunci da mulkin mallaka na babakere da Isra'ila tayi wa Palastinu.Sannan labari ne sananne ta yadda kasar Isra'ila ta jera shekaru tana karkashe Palastinawa mata da yara da tsofaffi,tare da rusa masu gidaje da gonaki da makarantu da asibitoci da wuraren sana'a da tilastawa dubun dubatan Palastinawa hijira zuwa wasu kasashe .Duk da irin zaluncin keta da ta'asar da Isra'ila keta aikatawa har yanzu ,kasashen dake da'awar 'yanci da kare hakkin dan-adam da dimokaradiya ke tallafawa Isra'ila da bata cikakken kwarin gwiwa kan abinda take aikatawa na assha ga al'ummar Palastinu musamman kasar Amerika.

Ranar Kudus rana ce ta masoya yanci da adalci da zaman lafiya da daidaituwa da mutumta hakkin dan-adam a ko'ina cikin duniya wadanda suke nuna goyon bayan su ga Palastinawa da ake zalunta da kuma kokarin isar da sakon halin kakani-kayin da Palastinawa ke ciki ga wadanda basu sani ba ko kuma suka jahilci halin da Palastinawa e ciki a hannun kasar Isra'ila .Kuma ranar Kudus ta kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tunatar da kawunan su cewa Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas baya karkashin kulawar su da ikon su.Kazalika Ranar Kudus ta kasance ranar da kusan shekaru ashirin al'ummar Musulmi dake da wayewa ta siyasar duniya dama wadanda ba Musulmi ba da suka tsani zalunci da danniya ke isar da sakonni ta hanyoyin da yafi yi masu sauki na isar da sakon su na Allah -wadai ga kasar mamayar Isra'ila da nema wa Palastinawa da ake zaluntagoyon baya domin al'ummar duniya su tallafa masu.

Ranar Kudus ta kasance rana ta musamman saboda ta kasance ranar da ake sake jaddada goyon baya ga al'ummar Palastinawa wanda Musulmin duniya keyi harma da masoya 'yanci a ko'ina cikin duniya.Ranar Kudus rana ce ta sake samun natsuwa a zukatan Musulmin duniya da Palastinawa kan sanin cewa dole wata rana Kudus ta komo hannun Musulmi da Palastinawa.

Mu rika tunawa da Ranar Kudus ta hanyoyin da zamu iya koda kuwa yaya yake domin mu nuna wa al'ummar Palastinawa da ake zalunta cewa muna tare da su, su kuma kasar mamaya ta Isra'ila su san da cewa bama goyon bayan ta'assar da suke aikatawa sannan muna Allah-wadai da zaluncin da suke aikatawa.Sannan mu sake jaddada muhimmancin Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas ga Musulmin duniya.

Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

LET THE COURTS DECIDE YAR'ADUA'S LEGITIMACY

Delivering his speech after been sworn-in as President and Commander in chief,Alhaji Umaru Musa Yar'adua admitted that the election that saw to his position was flawed.Also the reports of both local and international observers and reactions of opposition parties clearly stated that the election was sub-standard and lacked the proper procedure of accepted election.

Opposition parties and candidates that contested under their platforms did the accepted form of protest,which is laying their grievences before the election tribunals rather than inciting their party members and supporters to take the law into their hands.By this,the opposition received applause as this action of theirs potrayed them as peaceful and law abiding ,and they also became vigilant,as some politicians want to take advantage of the situation to hold on to power.

Former President Olusegun Obasanjo and Chairman of INEC Prof. Maurice Iwu are of the opinion that the election is a job well done and on the other hand the reports of observers,who reported that the April elections was the worst ever in the whole world.It is only the courts that will decide who is the liar between them!

Events unfolding after the April elections with regards to the opposition parties are disheartening and shameful especially with regard to opposition ANPP. Firstly ,the party came out loud and clear during and after the April elections that the election was massively rigged ! And later they changed gear by accepting to par take in goverment of national unity eventhough they had filed a suit against the presidential election!! Lastly they withdrew their suit against the presidential election in total disregard to the yearnings and aspirations of their supporters who underwent untold sufferings and hardships in the name of national unity!!!

Also information available indicates that the opposition AC and it's presidential candidate Alhaji Atiku Abubakar had been under pressure to also withdraw their suit against the presidential election .Will they also succumb to pressure and change their position by withdrawing their suit against the presidential election?

Still on the issue of withdrawing the presidential suit from courts,the media featured the news of attempt to convince General Muhammadu Buhari to withdraw his suit against the PDP,Alhaji Umaru Musa Yar'adua and Dr. Goodluck Jonathan.The delegation was led by former President Alhaji Shehu Shagari ,Galadiman Katsina Justice Mamman Nasir,Chairman First Bank Alhaji Umaru Mutallab and former chairman of defunct Democratic party of Nigeria (DPN)Alhaji Saleh Hassan,where they discuss extensively with General Buhari on the need for him to withdraw his suit in the electoral tribunal in the intrest of Northern and National unity.On the part of General Buhari he informred them on his determination to continue with his suit in the election tribunals.

Am of the opinion that pressure ,threat and intimidation should not be used on opposition parties and their flagbearers to to withdraw their suits in the election tribunals.,as it would not augur and speak well of our democracy .It is a must on us Nigerians to show the world our determination and sincerity in the process of building a sound and durable democracy in our country eventhough some individuals did what they did during the April elections.Nigerian policicians never learn from history and as such let us allow the courts to do their jobs as verdicts passed will serve as deterrant to future elections.Up coming politicians will also learn the process of how to legitimately become leaders and representatives of their people.

To President Umaru Musa Yar'adua, if those parading themselves as negotiators for pressuring ,intimidating and threatening the opposition parties and their flagbearers to withdraw their suits in courts are doing on your behalf ,Sir, you should stop them ,as it would send a bad signal to Nigerians and International community that your reforms on the electoral process are nor sincere.And Mr.President ,why are you afraid?There seems to be only two options now left which are either the courts to legitimise your election or to nullify the election.If Nigerians are satisfied with the way you conduct the affairs of this nation in the few months you ruled ,they will massively vote for you!

The massively rigged April elections and suits in election tribunals superceded the issue of Northerness,tribalism,religious sentiment and sectionalism.It is an issue of justice and providing exempleanery history for unborn Nigerians .It is also a must for us as Nigerians to ensure that process of assuming the mantle of leadership is constitionally followed for enshrinement of justice ,unity and purposeful leadership.

Eventhough many Nigerians are of the view that in the few months that President Yar'adua ruled Nigeria he has been able to achieve alot in such a short period,among his achievements are availability of fuel in all filling stations nationwide at a uniform price,revoking the sales of Kaduna and Port-Harcourt refineries,revoking of so many contracts that were not properlyawarded by the previous Obasanjo administration,stopping the mass sacking of the Nigerian workers and even returning many to their duty post e.t.c. With so many achievements in few months ,it still did'nt stop many from within and outside the country to continue to regard his goverment as illigitamate! President Yar'adua can only legitimise his goverment through the courts.All those seeking the opposition parties and their flagbearers to withdraw their suits from courts are not sincere advisers to President Yar'adua! It is only the final verdict of the courts that can place Yar'adua's goverment in it's proper position.

General Buhari has today remained the only true democrat standing! He should be aware that the struggle he is into of strenthening our democracy and the rule of law is appreciated and suported by all true lovers of democracy .And Buhari has reached a special stage where he has now occupied an exalted seat in the hall of fame of true democrats ,not only in Nigeria but in Africa as a whole.General Buhari should continue with his case in the election tribunal up to the supreme court without succumbing to pressure,threat,intimidation and blackmail ,as his suit is on behalf of the Nigerian masses.

Opposition parties that have joined the goverment of National unity and those that have withdrawn their suit in the presidential election had deceived and betrayed their members and supporters.They should be aware that history has prepared for them a special place and their parties may meet the fate of AD !

Nigerian masses should resist any attempt to turn their country to a one-party state,and should not be tired in any way in the struggle to place Nigeria among the nations where free and fair elections could be obtained.A new Nigeria that all will be proud of especially the black race all over the world.

Politicians in all political parties that have filed suits in the election tribunals should continue pursuing their cases and that of their supporters uptill the supreme court.It is a collective must on all Nigerians to ensure that our country earns respect and prestige in the world political arena.


Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Tuesday 18 September 2007

A BAR KOTUNA SU HALASTA ZABEN YAR'ADUA

A jawabin da Alhaji Umaru Musa Yar'adua yayi bayan rantsar da shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya ya fito karara ya amince da cewa an sami kura-kurai a zaben daya kaishi ga zama shugaban kasa .Sannan kuma rahoton kungiyoyin sa-ido da martanin da jam'iyyun adawa suka bayar bayan zaben na watan afrilu na nuni da cewa basu gamsu da zabubbukan ba.

Jam'iyyun adawa da yan takara a karkashin jam'iyyun nasu sun yi abinda ya dace , wato maimakon yanke wa kansu hukunci ta hanyar tunzura magoya bayan su , su tada zaune tsaye sai suka shigar da kararaki a gaban kotunan zabe dan neman abi masu kadin hakkin su dana magoya bayan su .Kuma wannan mataki da suka dauka ya janyo masu yabo da sam barka domin ya nuna cewa suna son zaman lafiya da kishin kasar su da toshe duk watav kofa da wasu zasu cimma burin su na siyasa.

Duk da ikirarin da tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta (INEC)Farfesa Maurice Iwu keyi na cewa zabe sam barka da kuma rahoton kungiyoyin sa-ido dasu kuma suka bada bayanan cewa ba'a taba zabe mai muni ba a duniya kamar zaben Nijeriya na wannan shekarar.To ko a nan akwai bukatar kotu ta fayyace mana tsakanin su , su wanene makaryata!

Abubuwan dake ta faruwa a kasar nan tun bayan zabe ta bangaren jam'iyyun adawa nada ban takaici musamman ta bangaren jam'iyyar adawa ta ANPP. Da farko suka fito sukayi babatun cewa an atafka magudi suka dawo suka karbi goron gayyata na shiga gwamnatin hadin kan kasa duk da cewa sun shigar da kara a gaban kotu .Sai gashi sun janye karar da suka shigar a kotu kan zaben shugaban kasa ba tare da duba irin halin matsi da takura da magoya bayan su suka shiga ba da sunan cewa dan kasa ta zauna lafiya.Haka ma bayanai nata zuwa na cewa jam'iyyar AC da dan takarar shugaban kasar ta Alhaji Atiku Abubakar na fuskantar matsin lamba kan cewa suma su janye karar da suka shigar kotu.Ko suma zasu yi amai su lashe ?

Kan dai batun janye kararaki a gaban kotunan zabe ,kafofin watsa labarai sun ruwaito yunkurin shawo kan Janar Muhammadu Buhari ya janye karar sa dake gaban kotu kan batun magudin zabe da ya gurfanar da jam'iyyar PDP da Alhaji Umaru Musa Yar'adua da Dakta Jonatan Goodluck .Inda bisa jagorancin tsohon shugaban kasa Alhaji Shehu Shagari da Galadiman Katsina mai sharia Mamman Nasir da shugaban bankin First Bank Alhaji Umaru Mutallab da kuma tsohon shugaban rusheshiyar jam'iyyar DPN Alhaji Saleh Hassan suka yi zama na musamman da Janar Buhari domin shawo kan sa ya janye karar sa dake gaban kotu ,saboda suna ganin cewa ta haka za'a sami hadin kai da zaman lafiya a kasa.Ta bangaren Janar Buhari bai yi kasa a gwiwa ba wajen sanar dasu cewa zai cigaba da bin kadin shari'ar sa.

Ni a ganinav bai kamata ana tursasawa jam'iyyun adawa da yan takara su janye karar da suka shigar kotu ba.Yin haka tawaya ne ga tsarin dimokaradiya .Dole ne mu nuna wa kasashen duniya cewa da gaske muke bisa da'awar bin tsarin dimokaradiya duk da abinda wasu suka aikata a lokacin zaben wannan shekarar.Yan siyasar Nijeriya basa daukan darasi da yiwa kansu fada,amma in shari'a tayi aikin ta ,to zai zama darasi ga yan baya gun ganin cewa sun bi hanyoyin da suka dace dan zama shugabanni da wakilan al'umma.

Ina kuma kira ga shugaban kasa Alhaji Umaru Musa Yar'adua , da in da bazar sa ake rawa wajen kokarin ganin cewa an shawo kan yan adawa su janye kararakin su dake gaban kotu ,to lallai ya tsawatar ya kuma hana saboda zai nuna cewa bada gaske yake ba kan gyara batun zabe da kuma kokarin sa na tsabtace harkokin zabe. Kuma tsoron me yake ji ! Cikin biyu dole a yi abu guda wato ko kotuna su tabbatar da zaben sa ko kuma su rushe zaben suce a sake ,in yan Nijeriya sun gamsu da ayyukan da yayi a watannin da suka gabata sai su zabe shi !

Zancen magudin zabe da kararakin dake gaban kotuna sun shige zancen Arewaci ko Kabilanci ko Bangaranci ! Zance ake kan tabbatar da adalci da samar da kyakyawar turba a tarihi yayin da yan baya zasu karanci tarihin kasar nan anan gaba Dole ne a dawo da tsarin samar da shugabanci bisa turban gaskiya da adalci da rikon amana.

Duk da cewa wasu yan Nijeriya na ganin cewa Shugaba Yar'adua yayi rawan gani a wasu fannonin a watannin da yayi bisa kujerar mulki kamar samar da wadatattcen man fetur a farashi bai daya da soke cinikin matatar man fetur na Kaduna da Fatakwal da wasu kwangilolin da basa bisa ka'ida a gwamnatin baya da dakatar da korar ma'aikata dama dawo da wasun su bakin aiki da sauran su. Duk wannan bai hana wasu a cikin gida da kasashen waje daina ganin gwamnatin sa a matsayin haramtacciyar gwamnati ba! Shugaba Yar'adua na iya samar wa gwamnatin sa halacci ne kadai ta hanyar kotuna!! Masu kaiwa da komowa domin ganin an janye kararakin ba masoya na gaskiya bane ga shugaba Yar'adua!!! Gaba tafi baya yawa dan tarihi ba zai kyale duk wanda dashi aka dafa aka sha a zaben wannan shekarar ba sai in har kotu ta zartar da hukuncin ta.

Janar Buhari a yau ya kasance gwarzon dimokaradiya shi kadai tilo,ya san da cewa gwagwarmayar da yake yi na gyara al'amurran dimokaradiyya a Nijeriya a yau duk masoya cigaban dimokaradiyya na gaskiya na tare da shi .Kuma ya san da cewa ya taka matsayi na musamman a farfajiyar bunkasar dimokaradiya ba'a Nijeriya kadai ba a'a a Afrika gabaki daya.Kada ya ja da baya ya bi kadin shari'ar da ya shigar a madadin talakawan Nijeriya har kotun koli ta kasa!

Jam'iyyun adawa da suka shiga gwamnati da wadanda suka janye shari'ar da suka shigar kotu su san da cewa sun ci amanar yan jam'iyyar su da magoya bayan su.Su kuma sani cewa lallai tarihi ya tanadar masu inda zai ajiye su,kuma tabbas su saurari makoma irin ta jam'iyyar AD!

Ga talakawan Nijeriya kada mu taba yarda a maida kasar mu mai bin tsarin jam'iyya guda, kuma kada mu gaji da gwagwarmayar sai kasar mu ta shiga sahun kasashen da ake zabe na gaskiya da amana ,kasar mu ta kasance abun koyi ga kasashen Afrika da abin alfahari ga bakaken fata a ko'ina cikin duniya.

Yan siyasa a kowane jam'iyya da suka shigar da kara a kotu su cigaba da bin kadin hakkokin magoya bayan su har kotun koli.Dole ne mu hada karfi da karfe wajen dawo da martaba da mutumcin kasar mu a idon kasashen duniya.

Haza wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com