Thursday 28 June 2007

SARAKUNA DA MALAMAN ADDINI SUNA TARE DA TALAKAWA KUWA?

A jerin shugabannin al’umma a kasar mu Nijeriya ,Sarakuna da Malaman Addini nada matsayi da martaba na musamman kasantuwar su iyayen al’umma.Sun kasance fitilu masu haskakawa al’umma hanya kan yadda zasu tafi da rayuwar su bisa tsari da tarbiya kan tafarkin da sukayi imani dashi.Kuma sun kasance masu umarni ga al’umma kan aikata kyawawan aiyuka da gujewa munanan aiyuka.

Talakawa na matukar girmama su da amsar umarnin su saboda imanin da suke dashi na cewa baza su so duk wani abin da zai cutar da su ba.Amma sabanin irin rawar da sarakuna da malaman addini suka saba takawa, a yau mun wayi gari wasu daga cikin su sun sake salon tafiyar su ta wajen kasancewa tare da masu mulki da masu hannu da shuni.A yau a bayyane yake wasun su sun raba gari da talaka ,sun shiga tawagar masu mulki da masu hannu da shunin da suka dora kasar nan bisa tafarkin jari hujja da tsarin su talaka shine makiyi abin ki,saboda tsare tsaren su da manufofin su a kullum sai kara jefa talaka cikin halin kakani kani da bakar wahala suke kara tsunduma talaka.

Malaman addini a ko’ina cikin duniya an shaide su da a kullum da kasance tare da gaskiya kuma kira ga mabiyan su kan kamanta gaskiya da rikon amana .Basa tsoron fadin gaskiya komai dacinta .Sannan kuma basa hada kai da azzalumai da yan handama da masu halin fataken dare.Littatafan tarihin addini a cike yake da gwarazan malaman da sukayi kira da a daina zalunci,har ma wasun sun jagoranci al’umma ga kawar da zalunci da kama karya.A zamanin nan da muke ciki a idanun mu mun gan ko jin labaran malaman addinin da suka murkushe zalunci da azzalumai,dama malaman da aka daure su,ko aka tilasta masu gudun hijira ,koma aka raba su da rayukan su ba dan komai ba sai dan suna hani ga zalunci da danniya da wasu kalilan mutane suke yiwa mafi rinjayen mutane dan kawai tsarin tursasa al’umma na hannun su.

An wayi gari wasu malaman addini suna fassara littafan addinan su bisa tafarkin da zasu da’da’da wa masu mulki rai dan su sami abin duniya.Mun wayi gari in kayi fashin mulki ko magudin zabe zasu ce Allah ne ya baka! In ka saci dukiyar al’umma zasu ce Allah ne ya azurta ka!! In ka tursasa al’umma da karfin tsiya kan abinda sukayi intifakin basa so zasu ce Allah yace a bika!!! Kuma a yau mun wayi gari wasu malaman addini sune a kullum kan hanyar gidajen gwamnatocin jiha da tarrayya da gidajen wadanda kowa yasan ta hanyar da suka tara dukiyar su.

Ba wai ina cewa laifi bane ga sarakuna da malaman addini suyi mu’amala da masu mulki da masu hannu da shuni bane a’a matsalar shine na basa iya fada masu hakikanin gaskiyar halin da talakawa da kasa ke ciki.Talakawa na shan bakar wahalan da basu taba sha ba tun kafuwar kasar nan Nijeriya.Babu aikin yi da rashin magunguna a asibitoci da rashin wutar lantarki da rashin da babun suna da yawa.Amma wasu sarakuna da malaman addini sun tsuke bakunan su ,sun wayan ce kamar komai na tafiya dai dai! Kullum suka buda bakunan su sai kan talaka,sarakuna su fadawa talakawa su zauna lafiya ba tare da fadawa masu mulki suyi adalci ba, malaman addini kuma wa’azin su a kan talaka sukeyi kan ya daina kaza babu kyau ba tare da fadawa masu mulki su daina jefa talaka cikin matsi ba.
Babu ja kan cewa sarakuna da malaman addini suna da matsayi da martaba na musamman a al’ummar kasar nan.Shin matsayin da martaban bai ishe su bane suke tarewa a gindin masu mulki?Sannan akwai wani abin duniya da suka rasa shi yasa suka zama maroka ga masu mulki?Suna tsammanin kan mutane bai waye bane har yanzu suke fadin son zuciyar su a matsayin umarnin addini?Suna zaton cewa bin son zuciyan masu mulki shi zai kare masu kujerun su?Kuma sai a yaushe zasu samar wa kansu yanci a daina kiran su yan amshin shatan gwamnati?

A shugabannin al’umma a yanzu sarakuna da malaman addini ne kawai suka rage da talakawa kewa kallon da kyakyawan zato saboda imanin da suke dashi na cewa zasu yi masu jagoranci na gari da kare masu hakkokin su da samar masu kyakyawan yanayin da rayuwar su zata kasance cikin sauki da walwala.Shin ba babbar cin amana bane a ce a yau a matsayin su na jagorori sufi damuwa da samun biyan bukatun kan su kan na mabiyan su?Basa tunanin cewa talakawa na kallon su ,suna kuma iya yi masu irin nasu fassaran ,kuma masu iya magana na cewa mutumci madara ne in ya zube baya kwasuwa duka.

Tarihin kasashen turai da wasu a Asiya ya nuna irin rawar da sarakuna da malaman addini suka taka a baya. Me ya kawo karshen tasirun su a yau?amsa a bayyane yake ,saboda dasu aka hada kai da baki ana zaluntar talaka ,sun hada baki da masu mulki da kuma guguwar juyin juya hali yazo sai yayi awon gaba dasu gabaki daya.Shi yasa a wasu kasashen ma gabaki daya babu burbushin tsarin mulkin sarautar gargajiya,su kuma malaman addini suka rasa tasiri a rayuwar al’umma kan umartan su da kyakyawan aiki da hani ga mumunan aiki.

Ina sarakunan da suka tsayawa ,tare da daurewa masu magudin zabe gindi kan su zauna daram a kujerun su na mulki a kasar nan suke?Abinda yaci doma ba zai bar awai ba!Kuma tarihin kasar nan tun jamhuriya ta farko zuwa yau,sarakunan da suka bada hadin kai wajen dorawa talaka wanda bashi ya zaba ba na karewa da murabus!Haka ma duk malamin addinin daya hada baki da masu mulki na rasa girma da kima a idon jama’a dan suna ganin sa a matsayin malamin gwamnati.

Martaban sarakuna da malaman addini na iya karuwa sosai in suka martaba bukatun talaka da kare hakkokin sa.Su sami manufar fadawa masu mulki gaskiya koda a gaban sune,tare da basu shawarwarin da rayuwan talaka zata inganta da kuma kiran su dasu daina cigaba da duk manufofin dake kara jefa talaka cikin matsi.In kuma suka ziyarci gidajen gwamnati daga kananan hukumomi zuwa na tarayya ya kasance bukatun al’umma ne ya kaisu bawai samar wa kamfanonin su da ya’yan su kwangiloli da mukaman gwamnati ba .Yanda suke iya fadawa talaka gaskiya ,su iya fadawa masu mulki gaskiya.Kuma ya kamata a koda yaushe su kasance cikin sahun farko na kira ga gwamnati su canza duk wata manufa da al’umma ke kukan zai matsa masu,ba wai wasu daban su kasance a sahun gaba ba wajen kwatowa talaka yanci.

Shugabani na gari abin koyi ne ga talakawan su .Duk shugaban da ya sace dukiyar al’umma ko a baya ko a yanzu ya zama wajibi ga sarakuna da malaman addini su san irin mu’amalar da zasu yi dasu ,saboda rungumar su a jiki ke bada kwarin gwiwa ga yan’baya kan cewa suma za’a rungume su idan suka bada kudi aka gina wuraren ibadu da kuma kai gaisuwa fada ayi masu sarauta.Talakawa na tare da sarakuna da malaman addini ,da fatan suma kamar yanda ake martaba su,zasu cigaba da kasantuwa da talakawa,domin sabanin haka na iya janyowa talakawa su daina ganin kimar su wanda ka iya zama barazana ga al’umma gabaki daya domin in babba ya tsawatar aka ki sauraran sa to wa ke iya wannan babban aiki na dora al’umma bisa tafarkin shiriya?


Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

No comments:

Post a Comment