Monday 16 June 2008

YUNKURIN JANAR JANAR NA WANKE ABACHA: IHU BAYAN HARI!

Ranar 8 ga watan Yuni, tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha ya cika shekaru goma da rasuwa. Kamar kowane shekara iyalan marigayi Janar Sani Abacha kan gabatar da addu’oi a irin wannan ranar . Amma abinda yafi jan hankali a addu’ar na bana shine haduwar tsofin shugabanin kasa na soja wato Janar Muhammadu Buhari da Janar Ibrahim Babangida da Janar Abdulsalam Abubakar, inda kowanen su ya fito karara ya karyata zargin da akeyi na cewa marigayi Janar Sani Abacha yayi rub da ciki da dukiyar al’umma yayin da yake mulki.

Kafofin watsa labarai sun ruwaito Janar Muhammadu Buhari na fadin cewa “dukkan zargin da akewa Janar Sani Abacha zai kasance zargi ne kawai”. Shi kuma Janar Ibrahim Babangida na cewa “ zargin da akewa Abacha basu da tushe balle makama…kuma babu kanshin gaskiya na cewa yayi almudahana da dukiyar al’umma”. A inda shi kuma Janar Abdulsalam Abubakar ke cewa “ abin takaici ne da rashin adalci a zargi iyalan marigayi Sani Abacha da satar dukiyar al’umma”.

Wannan yunkurin na Janar Buhari da Babangida da Abubakar na wanke marigayi Janar Sani Abacha daga zargin wawushe baitul malin gwamnati ya baiwa jama’ar kasa mamaki saboda basu fito sunyi wannan jawabin ba sai bayan shekaru goma da rasuwar sa. Duk da suna raye , suna ji , suna gani a lokacin gwamnatin baya da take ta shela tana sanar da duniya irin magudan kudaden da take karbowa a matsayin boyayyun kudade daga bankunan cikin gida da kasashen waje da marigayi Abacha ya boye.

Jaridar Thisday ta ranar 5 ga watan Yuni 2008 , ta larabto cewa kasar Switzerland ta fadi cewa ta maido wa gwamnatin Nijeriya dukkan kudaden sata da marigayi tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha ya boye a bankunan kasar ta , ba tare da wani sharadi na yanda za’a kashe kudaden ba. Jaridar ta ruwaito Ma’aikacin ofishin jakadacin na kasar Switzerland a Nijeriya , Mista Fabio Baiardi na cewa , sun maido wa Nijeriya kudade a kashi-kashi , yace a kashin farko sun bada dala miliyan 290 ranar 1 ga watan Satumba na 2005, sannan kashi na biyu sun bada dala miliyan 168 a ranar 19 ga watan Disamba na 2005, sai kashin karshe, dala miliyan 40 a karshen watan Janairu na 2006.

Bayanai na nuni da cewa Nijeriya tayi nasarar karbo dala miliyan 505.5 daga gwamnatin kasar Switzerland cikin kudaden da ake zargin Janar Sani Abacha ya sace tare da boye su a kasar kamar yanda bayanan da Ofishin majalisar dinkin duniya mai yaki da miyagun kwayoyi da laifuffuka da kuma bankin duniya suka bayar karkashin sabon yunkuri da ake kira da Stolen Asset Recovery (STAR ). Sannan ta bangaren gwamnatin Nijeriya anyi bayanin cewa an karbi kudi har dala miliyan 800 daga cibiyoyin hada-hadan kudi na cikin gida, cikin dala biliyan 3 zuwa 5 da ake zargin marigayi Janar Sani Abacha ya wawure, an kuma bada kiyasin cewa an karbi jimalar kudi dala biliyan 1.3 cikin kudaden.

In har zancen Janarori ya kasance gaskiya to ina kasar Switzerland ta sami miliyoyin dalolin data maidowa Nijeriya a matsayin kudaden da marigayi Janar Sani Abacha ya boye a bankunan kasar ta? Sannan ofishin majalisar dinkin duniya da bankin duniya ina suka sami bayanan da suka bayar kan kudaden da aka karbo na marigayi Janar Abacha? Su kuma (Janarori) ina suka sami nasu bayanan na cewa Janar Sani Abacha bai wawuri dukiyar Nijeriya ba?

Abin tambaya a nan shine me suke so su cimma da wannan furucin nasu na wanke Janar Abacha bayan shekaru goma ? In har tsofin shugabanni uku sun isa su bada sheda na wanke wanda ake zargi, to lallai sai yan Nijeriya su amince da shedan da tsofin shugabannin kasa uku wato Janar Yakubu Gowon da Alhaji Shehu Shagari da Cif Earnest Shonekan zasu bayar kan tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo kan yanda ya tafiyar da dukiyar Nijeriya daga 1999 zuwa 2007.

Yan Nijeriya na bukatar sanin gaskiyar lamari game da zargin satan dukiyar kasa da gwamnatin baya ke zargin marigayi Janar Sani Abacha dayi. Tunda har Janarorin sun fito a yanzu su shedi cewa Janar Abacha bai saci dukiyar al’umma ba, sai su kara wa yan kasa haske dan suyi watsi da bayanan da suka fito daga kasar Switzerland a matsayin kazafi ga marigayi Janar Sani Abacha.



Shehu Mustapha Chaji

shehuchaji@yahoo.com

Tuesday 10 June 2008

Kano 2011: Da sassafe ake kama fara

Ba’a bori da sanyin jiki, da alamun wannan Karin Magana ke sa yan siyasar jihar Kano dake da burin gadar gwamnan jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau bayan ya kamala wa’adin mulkin sa a zango na biyu keta shirye-shiryen ganin ko zasu dace. Wasu cikin masu kokarin ganin cewa sun gaji Gwamna Shekarau tuni suka fara nuna kansu ta hanyar kaddamar da kamfen ta bayan gida ta hanyoyin da suke ganin yafi dacewa a gare su dan samun goyon bayan al’ummar jihar Kano.
Cikin sahun gaba na masu son shige gidan gwamnatin jihar bayan Gwamna Shekarau ya nade kayan sa a shekarar 2011, sune yan jam’iyyarsa ta ANPP . Sannan yan jam’iyyun adawa musamman yan jam’iyyar PDP , sai kuma yan jiran ganin yadda guguwar siyasar zata kada kafin nan da shekarar 2010.
Mafi yawan yan takarar gwamnan jihar Kano dake nuna kansu ko kuma suke da niyyar tsayawa takara a shekarar 2011 in Allah ya kaimu sune manyan jami’an gwamnati da gaggan yan jam’iyyar ANPP me mulki a jihar. A sahun gaba na masu neman mukamin gwamnan a jihar sune Aljaji Sani Lawan Kofarmata, limamin Allah ya maimaita, Darakta Janar na Hukumar alhazai na jiha da Injiniya Abdullahi Muhammad Gwarzo mataimakin gwamna da Alhaji Garba Yusuf na hannun daman Gwamna Shekarau kuma kwamishina a gwamnatin sa da Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso kwamishinan raya karkara kuma kakakin jam’iyyar ANPP na jihar Kano da Injiniya Sarki Labaran kwaminishan aiyuka da Alhaji Abdullahi Sani Rogo .
Kazalika Sanatocin jihar a majalisar dattijai na kasa wato Sanata Kabiru Gaya da Sanata Muhammad Bello da Sanata Aminu Sule Garo ba’a barsu a baya ba wajen ganin cewa ko zasu dace su gaji Gwamna Shekarau ba. Tun dawowar tsarin dimokaradiya a shekarar 1999 tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Kabiru Gaya keta hankoran ya sake komawa gidan gwamnatin jihar amma hakar sa bata cimma ruwa ba. In da rai da rabo, ba shakka kila ya sake jarraba sa’ar sa a zaben 2011. Shi kuma Sanata Muhammad Bello tun shekarar 2003 yake ta kokarin ganin cewa ya shige gidan gwamnatin jihar, kuma tun dawowar sa jam’iyyar ANPP yake ta kokarin ganin cewa ya sami gindin zama kuma hakan yasa yayi taka tsan-tsan wajen kaucewa karo da Gwamna Shekarau duk da radi-radin da ake tayi na cewa yana da sha’awar kujerar gwamnan jihar kafin zaben 2007.Shima ana ganin cewa tunda gwamna Shekarau zai bar mulki a shekarar 2011 to shima zai jarraba farin jinin sa ga al’ummar jihar Kano ganin yadda ya shafe shekaru yana yi da dukiyar sa wajen karfafa jam’iyyar ANPP a jihar da taimakawa jama’a da kungiyoyi a jihar. Shi kuma Sanata Aminu Sule Garo tun kafin zaben 2003 yake da sha’awar fitowa takarar gwamnan jihar Kano amma a lokacin abokin sa Alhaji Ibrahim Amin Little ya sha gaban sa a lokacin .Shima da alamun wannan karon zai sake yinkurawa ko zai dace a wannan karon. Sai dan majalisar tarrayya Alhaji Danlami Hamza wanda a yanzu yana zango na uku a majalisar yana cikin wadanda suke da sha’awar zama gwamna a 2011.
Suma wadanda suka canza sheka daga wasu jam’iyyun zuwa jam’iyyar ANPP ba za’a bar su a baya ba wajen neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar ANPP ba a shekarar 2011. Cikin su akwai Alhaji Barau Jibrin tsohon dan majalisar tarayya kuma na hannun dama a daga tsohon kakakin majalisar tarayya Alhaji Ghali Umar Na’abba da tsohon gwamnan jihar Kano Dakta Muhammadu Abubakar Rimi, sai Alhaji Shehu Yusuf Kura wanda yayi takarar gwamna karkashin jam’iyyar PDP da Dakta Bala Salisu Kosawa shima dan takarar gwamna karkashin jam’iyyar NDP.
Ta bangaren jam’iyyar PDP me adawa a jihar Kano wadanda ake ganin zasu shiga sahun gaba a takarar sun hada da Alhaji Ibrahim Amin Little da Alhaji Ahmed Garba Bichi ministan kasuwanci da Alhaji Ghali Umar Na’abba tsohon kakakin majalisar tarayya da Dakta Shamsudeen Usman ministan kudi da Alhaji Faruk Lawan dan majalisar tarayya da Alhaji Aminu Dabo da Alhaji Usaman Sule Ruruwai dan takarar jam’iyyar A.C a zaben 2007.
Ta bangaren magoya bayan Janar Muhammadu Buhari a jihar Kano suma zasu fito da karfin su saboda da zarar abinda suke jira ya tabbata na matsayin da Buhari zai dauka bayan hukuncin kotun koli zasu kara kaimi wajen ganin cewa dantakarar gwamnan jihar Kano da zasu mara wa baya mai goyon bayan Janar Buhari ne.Burin magoya bayan Janar Buhari a jihar Kano karkashin jagorancin Alhaji Haruna Ahmadu Dan Zago shine na samin gwamna me goyon bayan Janar Buhari a jihar Kano a shekarar 2011.
Sai dai da alamun cewa takarar na gwamnan Kano a shekarar 2011 zai iya zuwa da sarkakiya in har ta tabbata Gwamna Ibrahim Shekarau ya canza sheka zuwa jam’iyyar PDP kafin zaben 2011 , inda ko yayi nasara wajen tsaida magoya bayan sa a takara har dana gwamna yanda tsohon gwamnan jihar Kebbi SSanata Adamu Aliero ya sami nasarar yi bayan ya koma jam’iyyar PDP ko kuma ya sami nakasu kamar yanda tsohon gwamnan jihar Jigawa Sanata Saminu Turaki ya samu inda yan jam’iyyar PDP na asali karkashin jagorancin Gwamna Sule Lamido suka mamaye takarar da mukamai masu tsoka suka sha gaban Sanata Saminu Turaki . In har ta tabbata Gwamna Shekarau ya koma jam’iyyar PDP jam’iyyar zata kwashi ruguntsumin banbancin ra’ayi tsakanin gaggan jam’iyyar inda zai sami Tsohon gwamna Rabiu Musa Kwankwaso da tsohon gwamna Abubakar Rimi wanda kowannen su zai yi kokarin ganin cewa dan takarar sa na gwamna ne ya sami tikitin tsayawa takarar gwamna. Sannan akwai yan takara masu jinni a jika kamar su Alhaji Ibrahim Amin Little da Alhaji Ghali Umar Na’abba da zasu yi kokarin tabbatar da ikon su saboda kada ayi masu sakiyar da babu ruwa kamar yanda akayi masu a zaben fidda gwani na shekarar 2007.
Yanda Gwamna Shekarau ya tafiyar da gwamnatain sa a shekaru biyu masu zuwa zai iya bashi damar ko rashin damar tsaida tsaida wanda yake so ya gaje shi a shekarar 2011. Jam'iyyar sa ta ANPP a kasa na fuskantar durkushewa gaba daya saboda rigingimun cikin gida ga kuma barazanar mamayar PDP data tinkaro yankin Arewa maso Yamma yankin da Shugaba Yar'adua ya fito inda jam'iyyar keso ta tabbatar da ikon ta saboda Shugaba Yar'adua.
Al'ummar jihar Kano na lura da bibiyar yanayin siyasar dake gudana, in kuma Allah ya kaimu lokacin zasu duba su darge su dauki wanda suke ganin yafi dacewa ya jagoranci jihar a shekarar 2011. Ko su amince da duk wanda gwamna Shekarau ya nuna masu ko kuma su zabi wani daban albarkacin Shugaba Umaru Yar'adua ko kuma su sake amincewa da wanda Janar Muhammadu Buhari zai nuna masu kamar yanda yayi a shekarar 2003. Amma kuma ko su a kan kansu zasu duba wani daban a kan kansa da suke ganin shi yafi dacewa da cancanta dan samun romon dimokaradiya da ake ta tababa ko tsohon Gwamna Rabiu Kwankwaso da Gwamna Ibrahim Shekarau basu baiwa al'ummar jihar ba a lokacin mulkin su lokaci ne kadai zai bayyana.

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Tuesday 3 June 2008

After one year in office: President Yar’adua in the eyes of Nigerians

President Umaru Musa Yar’adua was exactly one year in office on 29-May-2008 as President of Nigeria. He came to power through an election that was alleged to be massively rigged according to reports of local and international observers. This led opposition parties to challenge his election in the courts and Nigerians are still waiting for the final verdict from the Supreme Court which can legitimize or nullify his election.

He assumed office in a situation that he needs the support of Nigerians as he was greeted by strike organized by the Nigerian Labour Congress(NLC) which demands him to reverse last minute policies of former President Olusegun Obasanjo who privatize Kaduna and Port Harcourt refineries, increase vat and price of petroleum. The policies were reversed as demanded by the organized labour which reflects the yearnings of Nigerians.

Saddle with the leadership of Nigeria President Yar’adua formulated the 7 point Agenda which according to him will be the central cardinal of what he wants to achieve so as to put Nigeria among the world emerging economies in the world. The 7 Point Agenda are Energy, Security, Wealth creation, Education, Land reform, Mass transit and Niger Delta. After one year in office did Nigerians feel the impact of the 7 point Agenda? And out of the 7 point Agenda which among is he able to addressed? How far has he gone in achieving the 7 point Agenda? Can Nigerians testify to any difference in his governance to that of previous administration of President Obasanjo?

Sincerely, Nigerians have not felt any impact on any of Yar’adua’s 7 point Agenda. Energy sector is getting worse than he met it, according to reports power generated by Egbin Thermal station with the capacity to generate 1,350 megawatts has drop to less than 800 megawatts. And Nigerians are still looking forward to Mr. President in fulfilling his promise of declaring the state of emergency in the power sector. Insecurity is on the increase as Nigerians continue to live in fair of activities of criminals. On the issue of Niger Delta, the militant youth had continued to disrupt oil exploration which led to drop in amount of oil drill every day from 2.4 million barrel to around 2 million.

Political analyst and commentators view the Yar’adua administration as slow and the government seem incapable of tackling the enormous problems affecting the country, couple with policies reversal and somersault. This had even led some to believe that Yar’adua’s administration is the continuation of Obasanjo’s administration as his government has achieved little in the past one year.

But one distinct quality of Yar’adua’s administration is in the area of rule of law. The President has tried in issues regarding to the rule of law compare to the previous administration of Obasanjo. In the past one year all court rulings were abide by the President especially verdicts that had affected governors of his ruling party. He has also promise to cease to be president if the Supreme Court annulled his election and hand over to who the court decide will take over.

Though the President Yar’adua has promise to bring about electoral reform, Nigerians have continue to experience massive election riggings and manipulations from local government elections to re-run elections conducted all over the country. He should also fulfill that promise so that Nigerians will have free and fair elections like all democracies in the world. Free and fair elections will encourage Nigerians to believe and trust democratic governance as a tool for social, economic and political development of their country. President Yar’adua should not allow Nigeria under his leadership to become a one party state as canvassed by his party men.

In the area of corruption, President Yar’adua is not been accused by Nigerians of embezzling their nation’s resources as previous administrations were accused. And there is no allegation of spreading corruption and bribery in the National Assembly to enable him have his ways as it was alleged during the past administration where Ghana must go bags are used to achieve personal and selfish interest .Also he is not accused of interfering with the running of affairs in the legislature and judiciary in process of executing their works.

Nigerians expects action and not lip service from Yar’adua’s administration, to execute projects that will better their lives. Lack of constant power has led to set back in the economic sector and he should boost the agricultural sector or to be short and precise, President Yar’adua should fully implement his 7 point Agenda as he has promised Nigerians.

Many Nigerians believed that President Yar’adua has good intention for Nigeria and Nigerians. Some are of the view that the court cases have been affecting his performance in office. President Yar’adua should side with the Nigerian people and what they want as trying to please somebody or some people will hinder him from implementing his dreams for Nigeria. Time does not wait as one year out of four is already gone.

If a national survey for public opinion will hold on rating the Yar’adua’s administration for the past one year , most Nigerians will express the opinion that Yar’adua’s administration have achieved less and it has failed in bringing about any positive impact on their lives. For Nigerians , their lives today has no difference from the past eight years they had lived under Obasanjo’s administration and they have started loosing hope that the Yar’adua’s administration will bring about any positive change in their lives.

In the next coming months Nigerians can access if the change they desire will come about or they will continue to live as they had lived in the past nine years which is suffering with all the billion of dollars the country is making due to high increase in oil price.

Shehu Mustapha Chaji

shehuchaji@yahoo.com