Wednesday, 12 February 2014

Origin Of Dandalin Siyasa Online Forum

Dandalin Siyasa was created on March 19, 2008 by Shehu Mustapha Chaji, with the aim of providing a forum that mostly Nigerians from Northern part of the country can discuss and debate on issues relating to politics. And to also provide them with a forum that they can express their views and opiniions in matters relating to promotion of democracy in Nigeria, Africa and the world over. Dandalin Siyasa online discussion forum is established to be a forum for gavel-to-gavel discussion of political development in Nigeria, Africa’s largest democracy. Culled from : Dandalin Siyasa (An online discussion forum) in promotion of democracy and good governance in Nigeriafrom 2008 to 2010

Monday, 16 December 2013

Rahoto: Yadda Taron Dandalin Siyasa Ya Gudana A Zamfara

Al’ummar yankin Arewacin tarayyar Nijeriyar yau sun baje kolin hajar ra’ayoyinsu kan mabanbantan matsaloli, kalubale da kwan-gaba-kwan baya da ke addabar yankin wanda kai tsaye za a kwatanta da ukubobin mulki irin na gashin ragon layya da talakawa da al’ummar kasa ke fuskanta karkashin mulkin jam’iyyar PDP. Wannan ya biyo baya ne a babban taron Dandalin Siyasa na kasa karo na biyar da aka gudanar a Gusau birnin jihar Zamfara a makon da ya gabata a karkashin daukar nauyin Gwamnatin Abdul-aziz Yari Abubakar. A karshen taron bayan musayar ra’ayi, tattaunawa da gabatar da mukalu Dandalin Siyasa ya fitar da takardar bayan taro wadda ta yi bayani dalla-dalla kan matsayar da manbobin Dandalin suka cimma bakidaya. Taron tattunawa kan makomar kasa da Gwamnatin Tarayya ta kudiri aniyar gabatarwa ba zai samar da wata mafita ko wani gyara ga matsalolin da Nijeriya da ‘yan Nijeriya ke fuskanta ba. Dandalin ya ce taron ba ya da kowane irin alfanun da zai magance dimbin matsalolin da kasa ke fuskanta don haka suka yi kiran da a soke taron bakidaya. Bugu da kari Dandalin ya kuma yi magana kan manyan matsaloli da kalubalen da ke addabar yankin Arewa da suka had da; fatara da koma baya a fannin ilimi da tabarbarewar sha’anin tsaro da rashin cikakkiyar dama a lamurran siyasa. Haka ma wasu abubuwan da Dandalin ya cimma matsaya a kansu su ne; babu sadaukar da kai a siyasar Nijeriya, haka ma siyasar tana cikin mawuyacin halin da ke bukatar a sake daidaita lamurra. A kan wannan bayanin ya nuna bukatar da ke akwai ta zaben shugabanni nagari wadanda za su tafiyar da mulkin gaskiya a tafarkin gaskiya. Dakta Usman Muhammad, Malami a jami’ar Abuja shine ya karanta takardar bayan taron wadda a ciki kuma ta yi kira ga majalisar tarayy da ta yi fatali da batun dokar hukuntan wadanda ke suka da caccaka a dandalin sadarwa na zamani. A kan wannan bayanin ya yi kira ga masu shata dokoki daga yankin Arewa da kada su aminta a tabbatar da dokar. Baya ga wannan Dandalin ya bayyana cewar babu wani kwakkwaran amintaccen dan siyasa daya da ya samu karbuwa, goyon baya da amincewar jimlatan din al’ummar Arewa, wanda akan wannan bayanin ya nuna bisa ga bayyanar Dandalin Siyasa akwai kyakkyawan tsammanin Arewa da ‘yan Arewa za su samu ingantaccen dan takarar da zai samu karbuwa a yankin bakidaya. A jawabin da ya gabatar a matsayinsa na mai masaukin baki, Gwamna Yari ya bayyana cewar a bisa ga gazawar Gwamnatin tarayya wajen magance satar man fetur, da rabon tattalin arzikin kasa da ake yi yadda aka ga dama don haka taron tattaunawa na kasa da za a gudanar ba zai haifar da da mai ido ba ga siyasar Nijeriya. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ta bakin mataimakisa Ibrahim Wakkala. A nasa jawabin Gwamna Kwankwaso na jihar Kano shi kansa ya yi kakkausan kira ga al’ummar Arewa da su kauracewa Babban Taron na Kasa yana mai cewa “Ko kadan taron ba ya da wani amfani a garemu don haka muke kira da a kaurace masa. Baya ga wannan jagoran na Kwankwasiyya wanda Sakataren Gwamnatin jihar Kano, Rabi’u Sulaiman Bichi ya wakilta ya yabawa hobbasar kwazon Dandalin Siyasa na fadakar da shugabanni da jagororin siyasar yau kan halin ha’ula’in da al’ummar kasa suke ciki. Shugaban Dandalin Siyasa Hashimu Ubale Yusuf bai yi kasa a guiwa ba wajen bayyana yadda Dandalin ya kafu a 2008 da ‘yan manbobi kalilan, amma a yau bisa ga gamsuwa da abubuwan da ake tattaunawa an wayi gari akwai dubban manbobin Dandali na yahoogroups da nashafin Facebook. A taron an kuma aminta da karin wasu Manbobin Kwamitin Amintattu na Dandali ba ya ga wadanda ake da su. Wadanda aka tabbatar sune: Mataimakin Gwamnan Zamfara, Ibrahim Wakkala da Sakataren Gwamnatin jihar Kano, Rabi’u Bichi, da biyu daga cikin masu kula da Dandalin, Urwatu Bashir-Saleh da Uba Dan Zainab da Ahmad Sajo, daraktan yada labarai ga Gwamna Murtala Nyako na jihar Adamawa. Tun da fari gabanin ranar babban taron sai da aka fara kai ziyara a ranar jumu’a a gidan Kurkuku da gidan Marayu ta yadda Dandalin ya bayar da tallafin tufafi da kayan amfanin yau da kullum ga wadanda abin ya shafa domin tausaya masu ga halin da suke ciki tare karfafa masu guiwar samun kyakkyawar makoma a gaba. Kazalika domin neman albarkar masu albarka, haka ma an kai gaisuwar girma a gidan Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau. Baya ga wannan kuma a daren ranar babban taron, Gwamna Yari ya jagoranci cin liyafar musamman a fadar Gwamnatinsa a inda aka ci a ka kuma sha abincin alfarma a gidan alfarma a bisa ga bakuntar bakin mai alfarma. Baya ga wannan haka ma a ranar lahadi Kwamishinan yada labarai na jihar Zamfara Ibrahim Muhammad Birnin-Magaji ya jagoranci shugabannin Dandalin a ziyarar gani da idanu kan muhimman ayyukan raya kasa da ci gaban al’umma da Gwamnatin Shehi ta gudanar a Zamfara daga 2011 da ta fara jan zaren mulk zuwa yau. Wakilinmu ya ba mu labarin Dandalin Siyasa wani fitaccen Dandali ne da a farko aka asasa a yahoogroups a duniyar gizo inda jama’a da dama ke baje kolin hajar ra’ayoyinsu kan mabanbantan al’amurran da suka jibanci siyasa, zamantakewa da tattalin arziki, da sauran batutuwa da dama da suka shafi cigaban kasa da matsalolinta da ma hanyoyin magance su. Daga baya ne aka fadada shi ta hanyar buda shafin Facebook na Dandalin Siyasa. A haka ya zuwa lokacin hada wannan rahoton akwai manbobin Dandalin Siyasa na yahoogroups 1, 964 da kuma wasu manbobi 6, 733 da ke a shafin Facebook wadanda duka sun fito ne daga ko wane lungu da sakon Nijeriya, haka ma akwai manbobin da ke a sauran sassan kasashen duniya. Bugu da kari Dandali ya hada jama’a da dama daga jam’iyyun siyasa daban-daban, wadanda duka ke musayar ra’ayi tare da muhawarori masu ma’ana ba tare da amfani da zafafan kalamai kan wani ko wasu ba, kamar yadda dokar Dandali ta shata, a daya gefen tare da bin dokar kasa ta ‘yancin fadin albarkacin baki. A cikin Dandalin akwai zaratan shugabannin siyasa, ‘yan siyar akida, ‘yan siyasar zaure da ‘yan siyasar da ke iya azata ta zauna, baya ga manya, matsakaita, da kananan ma’aikatan Gwamnati, da ‘yan kasuwa, da masu mulki da masu iko da ‘yan Rabbana ka wadata mu, da dalibai da Malamansu da sauran mabanbanta al’umma maza da mata. Fassarar Sharafaddeen Sidi Umar da Hussaini Ibrahim, Gusau. Culled from Leadership Hausa

Bakuncin Gizago a Jihar Zamfara

Rabona da shiga cikin birnin Gusau na Jihar Zamfara tun mulkin Yariman Bakura na farko, kodayake na sha zuwa, amma dai shigar shantun kadangare nake mata, domin kuwa nakan wuce in je Sakkwato, ba tare da na shiga kwaryar garin ba. A wannan karon, na niki gari a ranar Juma’ar da ta gabata, na tunkari birnin. Babban makasudin zuwa Gusau kuwa shi ne, domin halartar taron ‘Dandalin Siyasa A Intanet’ karo na biyar, wanda Gwamnatin Jihar Zamfara ta dauki bakuncinsa. A matsayina na wanda ya dade bai rakade birnin Gusau ba, sai na samu kaina a matsayin bako, wanda haka ya sanya al’amura da yawa suka zame mani abin al’ajabi. Na farko dai, na samu garin ya canza matuka daga yadda na san shi a baya. Na ga yadda aka shimfide shi da manyan tituna masu gida biyu da magudanun ruwa a kowane bangare. Haka kuma, na ga yadda sababbi kuma manyan gine-gine suka cika birnin, kamar kuma yadda na ga an dandashe mahada titunan da fitulun ba da hannu. Game da hanyoyin nan kuwa, masu ababen hawa, musamman ma ’yan baburan Acaba, har ma da wasu masu motocin tasi, na ga yadda suke karya dokokin hanya kai tsaye. Na ga yadda suke yin tukin ganganci da wauta. Akwai lokacin da na zo shataletalen kusa da Gidan Gwamnati, fitilun bayar da hannu sun ba hanyarmu izinin tafiya amma sai ga shi ’yan Acaba da wasu kalilan din motoci sun shiga titi daga hannun da ke daura da namu (wanda kamata ya yi su tsaya). Bisa ga haka, saura kadan in kade wani mai babur amma Allah Ya kiyaye, na dauke kan motata da sauri. Da baicin taimako da agajin Allah, da yanzu labari ya cika gari, cewa Gizago ya kade dan Acaba, (Allah Ya kiyaye)! Wani abu kuma da ya daukar mani hankali game da Jihar Zamfara shi ne, yadda na rika jin mutane suna yaba wa gwamnatinsu mai ci a yanzu, a karkashin Gwamna Alhaji Abdul’aziz Yari Abubakar, musamman suna cewa yana yi masu ayyukan raya kasa. Da nake magana game da titunan da na ga sun kayata birnin, shi ne wani ma’aikacin otel din da na sauka ya shaida mani cewa ai duk aikin gwamnan ne mai ci yanzu. Al’amari na gaba da ya kara daukar mani hankali shi ne, abin da na tsinkaya a daren Lahadi, lokacin da aka gudanar da liyafar cin abincin dare tare da Gwamna Abdul’aziz Yari. An gudanar da liyafar ce a Gidan Gwamnatin Jihar Zamfara. Bayan an kammala cin abinci da abin sha, sai aka gayyaci gwamnan domin ya gabatar da jawabinsa. Jawabin nan nasa ne ya zama abu na gaba da ya doki zuciyata, ya daukar mani hankali matuka. Gwamnan ya bayyana yadda yake tafiyar da al’amuransa, sannan ya yi bayani dalla-dalla game da hakkin da ke kansa, kamar kuma yadda ya tunatar da al’umma cewa su ma suna da hakki. Ya ta’allaka yadda ake samun matsaloli da yawa daga shugabanni a Najeriya da rashin sanin makamar aikin da ke kansu. Ya ce a wannan zamani da muke ciki, mafi yawan masu rike da madafun iko, suna samun kansu ne kawai a mulki, ba tare da sun shirya masa ba. Game da haka, ya shawarci al’umma da cewa, duk wani abu da za su aikata, to su samu iliminsa tukunna. Mai mulki, ya yi kokarin sanin makamar aikin da ke gabansa. Wani kalamin da gwamnan ya yi, wanda kuma ya dauki hankalina, shi ne inda ya ce dole ne mai mulki ya yi taka-tsan-tsan da mabiyansa, wadanda a mafi yawan lokaci sukan wuce makadi da rawa wajen zuga shugaba, su nuna masa cewa shi ne shugaban kowa kuma ya fi kowa. Gwamnan ya ce, a lokacin da shugaba ya biye masu, ya dauki wannan zuga da ingiza-mai-kantu-ruwa, to zai kasance mai girman kai. Idan ya yi haka, to barna za ta biyo baya. Abu na gaba da ya daukar mani hankali a Jihar Zamfara, shi ne ganawarmu da Kwamishinan Watsa Labarai na Jihar Zamfara, zakakurin mutum mai himma, Alhaji Ibrahim Muhammad (dan Madamin Birnin Magaji). A matsayinsa na daya daga cikin jami’an gwamnati da suka kasance masu masaukin baki a taron nan, bai nuna gazawa ba ko kadan. Duk inda ake wata hidima a taron nan sai ka gan shi tsamo-tsamo, ana tafiyar da al’amura da shi. Saboda azamarsa, shi ya jagoranci membobin dandali da suka zo taron nan daga sassan kasar nan zuwa ziyarar gani da ido zuwa wasu muhimman ma’aikatu, domin shaida ingantattun ayyukan raya kasa da gwamnatinsu ta gudanar. Kwamishinan da kansa ya jagorance mu zuwa Gidan Rediyon Jihar Zamfara, wanda ake kira da sunan Gidan Injiniya Mamman Maru. Mun ga sababbin na’urori na zamani, wadanda aka shaida mana cewa su ne ake yayi a duk fadin duniya. A takaice, ya shaida mana cewa, gwamnatin Abdul’aziz Yari ce ta kashe kudi har Naira biliyan daya, wajen kammala ginin gidan rediyon da kuma inganta shi da wadannan na’urori na zamani. Ziyayar tamu ta dauke mu har zuwa Asibitin kwararru na Yariman Bakura, wanda shi ma aka inganta shi da na’urori na musamman, wadanda suka hada da na’urar gwajin yanayin sassan jiki, wadda da ita ake gwajin gano ciwon koda, ciwon suga da sauransu. Mun ga na’urar gwajin haihuwa ta zamani, mai aiki da hasken lantarki, wacce idan aka haska za a iya tantance yanayin ciki da sauran lalurorinsa. Mun ga na’urarori daban-daban, wadanda ya ce irinsu ne ake samu a manyan asibitocin zamani na kasashen duniya. Kamar yadda ya ce, duk wani awo da ake gudanarwa a asibitin, Naira dari biyar suke amsa, domin saukaka wa talakawa. Ya ce gwamnatin tasu, ta kashe sama da Naira biliyan biyu wajen kammala ginin asibitin da kuma inganta shi da na’urori. Daga nan ne kuma muka rankaya zuwa gadar boko, wadda kamar yadda Kwamishinan Watsa Labarai ya ce ake ginawa a halin yanzu. Wannan gada, hade da hanya mai nisan kilomita 75, za ta hada kananan hukumomin Talatar Mafara da Bakura da Maradun da Zurmi. Ya ce an bayar da kwangilar gina ta a kan Naira biliyan 7.1 kuma za a kammala ta cikin shekara uku, saboda muhimmancinta ga al’umma, musamman wajen bunkasa kasuwanci da noma da kiwo. Mun yi wa Kwamishina dan Madamin Birnin Magaji Tambayar cewa, ta yaya ake samun dinbin kudin da ake aiwatar da wadannan muhimman ayyuka? Shi ne ya amsa da cewa: “Gwamnanmu ya dakile duk wasu hanyoyi na almubazzaranci da dukiyar al’umma, yana ririta dan abin da ake samu daga Gwamnatin Tarayya.” Babu shakka na ji dadin bakunci na a Jihar Zamfara, musamman ma yadda na gana da Gizagawan Jihar Zamfara da na Jihar Sakkwato, su Yusuf Zamfara da su Kassim Lema da su M. A. Faruk da Nata’ala Babi da su Jamila Abubakar da Hussaina Abdullahi. Haka kuma, na hadu da zaratan Gizagawan Jihar Kaduna, irinsu Muntaka Abdul Hadi Dabo da Idris Barden Kubau da sauransu. Babu abin da zan ce, sai Allah Ya bar zumunci! Culled from Aminiya http://aminiya.com.ng/index.php/gizago/4053-bakuncin-gizago-a-jihar-zamfara

Bazazzagi da Larabci

Bazazzagi da Larabci Parent Category: Mu Sha Dariya Category: Mu Sha Dariya Published on Friday, 18 October 2013 00:00 Written by Aminiya Hits: 3856 Wani Bazazzagi ne suka hada kudi da Balarabe suka sayi jakai guda biyu suna kiwo. Kuma ya kasance Bazazzagi ke yin kiwon wadannan jakuna guda 2. Kwatsam wata rana sai aka yi ruwa ya cika gidan Bazazzagin nan, har jakunan suka mutu. Ya je ya samu Balarabe, yana so ya yi masa Bayanin cewa ruwa ya cika masa gida har jakunan sun mutu. Suna haduwa sai ya ce masa: “Wa himaruka wa himariy, al ma’u bulbula fiy baitiy, mautu jami’an.” Daga Shehu Mustapha Chaji Culled from Aminiya http://aminiya.com.ng/index.php/mu-sha-dariya/3385-bazazzagi-da-larabci

Jifar Shedan

Jifar Shedan Category: Mu Sha Dariya Category: Mu Sha Dariya Published on Friday, 25 October 2013 00:00 Written by Aminiya Hits: 3508 A wajan jifar shedan ne wani Bazzazagi da karambani sai ya ce shi a sama zai yi tasa jifar. Ga shi kato ne kuma baki kirin da shi, ga muni. Ya hau sama ya fara jifa ke nan sai jikkar kudinsa ta tsinke ta sullubo kasa. Gogan naku yana ganin haka, sai ya biyo abarsa suka yo kasa, yana kokarin sai ya cafki jikkarsa. Yana fadowa kasa, su kuwa alhazai sai suka ga kato a gabansu sai suka yi zaton shedan ne ya ji jifa ya bayyana a fili. Kawai sai suka ci gaba da antaya masa jifa, wasu ma har da takalmi; suna cewa: “Alugungumi, yau sai mun ga bayanka.” Shi kuwa sai ihu yake, yana cewa: “Ana insanun fi Zariya, Najeriya” (Ma’ana: Ni mutum ne dan Zariya, Najeriya). Da kyar wani Bakano ya cece shi! Daga Shehu Mustapha Chaji, Kano Culled from Aminiya http://aminiya.com.ng/index.php/mu-sha-dariya/3456-jifar-shedan

Yadda taron ‘Dandalin Siyasa A Intanet’ ya gudana a Jihar Zamfara

A ranakun Juma’a da Asabar da suka gabata ne aka gudanar da gagarumin taron ‘Dandalin Siyasa A Intanet.’ Taron, wanda ake gudanarwa duk shekara, shi ne karo na biyar a bana kuma an gudanar da shi ne a zauren taro na Jibrin Bala Yakubu da ke birinin Gusau, Jihar Zamfara. Tun a daren Juma’ar da ta gabata, bayan mahalarta sun gama sauka masaukinsu, sai aka taru a dakin taro na King’s City Hotel Gusau, inda aka gabatar da kwarya-kwaryan bikin maraba. Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Ibrahim Wakkala, ya halarci bikin da kansa. A nan ne ’yan wasan kwaikwayo na Hukumar Al’adu ta Jihar Zamfara suka gabatar da wasan kwaikwayo mai ilimantarwa. Wasan nasu ya fadakar game da muhimmancin da ke tattare da muhawara da tattaunawa game da al’amuran siyasa da kuma na al’amuran yau da kullum. Kafin sannan, wasu daga cikin membobi da shugabannin ‘Dandalin Siyasa Na Intanet’ sun kai ziyara zuwa babban gidan yarin Gusau, inda suka gaishe da fursunoni da kuma taya su alhini. Haka kuma, sun kai irin wannan ziyara zuwa Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke garin Gusau, inda suka duba marasa lafiya da gaishe su. Daga nan ne kuma suka rankaya zuwa Asibitin Yariman Bakura da nufin gaishe da marasa lafiya. Daga bisani kuma suka yada zango a fadar mai martaba Sarkin Katsinan Gusau, domin gaisuwar ban girma. A ranar Asabar kuwa, mahalarta sun yi wa zauren taro na Jibrin Bala Yakubu tsinke, inda nan ne aka gudanar da gagarumin taron, wanda ya fadakar, ya ilimantar kuma ya kayatar. A yayin gabatar da jawabinsa na maraba, Shugaban Dandalin Siyasa A Intanet, Alhaji Hashim Ubale Yusuf, ya bayyana jin dadinsa a madadin ’yan dandali, musamman ga Gwamnatin Jihar Zamfara, wacce ta kasance mai masaukin mahalarta taron. Daga nan ne ya zayyana muhimman ayyukan da dandalin ya gudanar. A taron dandalin na bana, masana sun gabatar da muhimman takardu har guda biyu, inda daga bisani mahalarta taron suka bijiro da sharhi da tsokaci da kuma tambayoyi. Takardar farko, mai taken ‘Arewacin Najeriya Da Batun Tattaunawa Game Da Taron Makomar kasa,’ Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa, babban malami a Jami’ar Bayero Kano ne ya gabatar da ita. Babban malamin ya yi tsokaci mai gamsarwa game da gazawar shugabanci a Najeriya, wanda haka ya haifar da matsalolin da suka hada da sace-sacen dukiyar gwamnati da hauhawar cin hanci da rashawa da sauransu da dama. Haka kuma, ya kawo misalan wasu daga cikin matsalolin da suka kawo wa Najeriya tarnaki, kamar tashe-tashen hankula da matsalar rashin tsaro. Bisa ga haka, ya ba da misali da ta’annatin tsagerun Neja-Delta da masu yin garkuwa da mutane don amsar kudin fansa, sannan kuma ya kawo misali da barnar da ’yan Boko Haram ke aiwatarwa a Arewacin Najeriya. Daga bisani kuma ya yi tsokaci na musamman game da ita kanta Arewa da matsalolinta da abin da ya kamata ta yi idan ta je wajen taron tattauna makomar kasa. Takarda ta biyu a wajen taron, Malam Nasiru Wada Khalil ne ya gabatar da ita, inda ya yi tsokaci tare da sharhi mai tsawo game da al’amuran kafafen sadarwa na intanet, musamman tare da kawo misalai daga majalisun yahoo na intanet a kasar Hausa ko kuma Arewa. Malamin ya bayyana dalla-dalla irin ci gaban da aka samu, a sakamakon amfani da wannan sabuwar fasahar sadarwa, wacce ta zama gama-gari a halin yanzu. Kadan daga cikin nasarorin sun hada da cewa fasahar intanet dai tana da tasiri da isar da sako cikin kankanen lokaci. Ta hanyar fasahar, al’umma suna kara wayewa da fahimtar inda aka sa gaba. Haka kuma ya bayyana cewa, ana isar da sako ga gwamnati, wanda kuma take fahimta da sauraro, saboda tasirin kafar ta intanet. Bayan kammala taron, an fitar da takardar bayan taro, wacce ta fitar da matsaya guda takwas, wadanda suka hada da: An bukaci gwamnoni 19 na Arewa da su dauki kwararan matakai domin magance matsalolin da ke addabar yankin. An bukaci al’ummar Arewa gaba daya, da su hada karfi da karfe, domin kawo karshen matsalolin tsaro da ke addabar yankin. Idan har yankin Arewa ya amince da ya shiga taron tattauna matsalolin kasa da ake shirin hadawa, to su hada kai su tafi da manufa guda daya. Taron ya bukaci kungiyoyin gama kai da makamantansu da su shirya gangamin wayar da kai domin fadakar da al’umma abin da ya kamata su yi, dangane da zabubbukan 2015 da ke tafe. An yi kira ga ’yan Majalisar Tarayya na Arewa da su yi tsayin daka wajen ganin ba a zartar da dokar nan da za ta dakile masu sukar gwamnati a intanet ba. Haka kuma, an yi roko na musamman ga Gwamnatin Tarayya da kuma kungiyar Malamam Jami’a Ta Najeriya, da su yi gaugawar kawo karshen yajin aiki da ake fama da shi a jami’o’in Najeriya, domin dalibai su koma bakin karatu. Dandalin kuma ya mika gaisuwar ta’aziyya ga kasar Afrika Ta Kudu saboda mutuwar dan kishin al’umma, Nelson Mandela. Daga karshe, dandalin ya mika godiya da yabawa ga Gwamnatin Jihar Zamfara, saboda daukar nauyin bakuncin taron, wanda ya zama gamsasshe. Taron ya samu halartar muhimman mutane maza da mata da suka hada da Shugaban Majalisar Tarayya, Alhaji Aminu Waziri Tabuwal, wanda Alhaji Abdulrahman Kawu Sumaila ya wakilta. Sai Alhaji Ibrahim Wakkala, Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara da Alhaji Hashim Ubale, wanda ya kasance Shugaban ‘Dandalin Siyasa A Intanet.’ An dai tashi taron lafiya tare da kudurin cewa za a gudanar da taro na gaba a badi, a Jihar Kano. Culled from Aminiya http://aminiya.com.ng/index.php/adabi/4019-yadda-taron-dandalin-siyasa-a-intanet-ya-gudana-a-jihar-zamfara

Tuesday, 10 December 2013

Congratulations to all Dandalites!

Congratulations to all Dandalites! Once again the Dandalin Siyasa Online Forum has proved to the world that it has finally come of age. It is now established that our great forum is now an institution and which we pray will outlive us and continue to contribute positively for the development and growth of our great country. The aim of this short letter is to apologize to the management and members of Dandalin Siyasa Online Forum my inability to intentionally miss our anniversaries, last year in Dutse and the latest in Gusau. It’s due to reasons many will come to understand in future. For two years before 19-March-2008 I had the idea of starting this great forum, but Allah’s time is the best and I created the forum on the mention date. I did it out of intrest of have such group in the North then. I never knew or predict it will be what is is today, and only Allah knows the greatness it will attain. The Dandalin Siyasa of yesterday is different from how it is today. In the past many regard the forum as my personal belonging, and that may be among the reasons some were against me, but with the present dandali which many I observed regard to “ours” has passed the stage of fighting the “Owner” or plotting against the leadership. With me out of the picture I think those fighting me in the name of dandali have no one to fight or plot against. The Great Dandalin Siyasa Online Forum, am using this channel to officially inform the leadership that I will be attending all Dandalin Siyasa Online Forum Anniversaries Insha Allah as it has been proved that its now an institution not a personal belonging of Chaji or an instrument to be used by him to further any kind of agenda from next year. From numerous comments I read, the youths, elites and even states governments from Northern Nigeria have hope in Dandalin Siyasa. They look toward dandali to provide the agenda for is good governance and democracy all about. Many now believe Dandalin Siyasa can chart the roadmap for growth and development in Northern Nigeria. I will also appeal to leadership of Dandalin Siyasa to be more patience and to also tighten its belt for future challenges as profile and influence of the forum is growing by the day. As humans we are bound to make mistakes and errors and when this happens, we should as usual forgive and forget for interest of our great forum, region and country. Once again a very big thank you to our great Chairman Pharm Hashim Ubale Yusufu, Engr. Sani Umar, Urwatu Bashir Saleh, Barr. Abdullahi Imam, Engr. Muazu Magaji, Nazeer Bello, Hon. Uba Danzainab, Hon. Binta Spikin, Mohammed Alhassan (BBS), Ahmed Salisu (ASI) Dr. Umar Tanko Yakasai, Mohammed Mansur Allawee, Saleh Dakata who all rose to keep the flag of Dandalin Siyasa flying in those trying period. I will remain gratefull to you all forever and continue to pray for your success and protections from all sorts of enemies. History will remember you and our people will continue to respect you forever. Many thanks to Zamfara State Deputy Governor Malam Ibrahim Muhammad Wakkala for all what he did to Dandalin Siyasafor successful 2013 annivesary. May Allah (swt) reward him abundantly and we pray that Governor Abdulazeez Yari will handover to him embracing each other. My appreciation to Engr. Rabiu Suleiman Bichi , SSG to Kano state government for identifying with Dandalin Siyasa, May Allah (swt) reward him abundantly, amen. My appreciations to all members of the Gusau 2003 Organizing committees, all members that attended the anniversary across the country, may Allah reward them abundantly. Once again a very big thank you to you all and I pray that ,all your needs in this world and hereafter will be fulfilled by Allah (swt). Thank You Shehu Mustapha Chaji Founder ( Dandalin Siyasa Online Forum)