Monday, 17 December 2007

LABARIN ZOMO DA MANGWARO

Wata rana ne Zomo na tsalle-tsallen sa yana tunanin zuci,daya karaso karkashin wata bishiyar Mangoro yana daga kansa sama sai ya hango wani Mangoro jajawur, ga girma kuma gashi ya nuna sosai.Ganin haka ya fara tunanin yaya zai yi ya sami Mangwaron dan shi ba zai iya hawa bishiyar ba. Yana tunanin yanda zai yi sai ga Kurciya ta sauka a kan bishiyar Mangwaron.Tana hango Zomo tayi masa sallama "barka dai "shima Zomo ya maida gaisuwar "kaima barka dai" Sannan ya kara da cewa "taimaka mani Kurciya ki tsinkar mani wancan Mangoron".

Kurciya a take ta tashi ta kusanci Mangwaron dan ta tsinka .Domin yawun ta ya tsinke da ganin mangoron kuma tayi tunanin ta cinye shi ita kadai. Amma da ta tsinki Mangoron sai ta kasa rikewa da bakin ta ,sakamakon haka sai Mangoron ya fado kasa.

Zomo na ganin haka cikin murna yac wa Kurciya"nagode" ya sun kuya ya dauki Mangwaro sai ya gan Mangwaron nata gungurawa daga gare shi , kai kamar Mangoron ne da kan sa ke gungurawa.Mamaki ya kama Zomo yana cewa" anya Mangoro da kansa zai yi ta gungurawa haka! Yana dubawa da kyau sai ya lura da cewa Mangoron ya fado ne a bayan Bushiya ya kuma makale a jikin kayoyin dake jikin ta. Shi yasa in ta motsa sai Mangoron ma ya motsa. Bushiya na ganin mangwaro a bayan sa ,ya yanke shawarar cewa Mangoron nasa ne kuma gashi da son Mangwaro. A take sai ya yanke shawarar ya arcen da Mangoron. Zomo na ganin haka ya kwada masa kira yana "tsaya! tsaya! dawo! Ina zaka da Mangoro na? Bushiya na jin haka sai ya samu waje ya tsaya, yace ma Zomo "Mangoron nan a baya na ya fado saboda haka Mangwaron nan nawa ne" . Kurciya na kallon su sai tace "kai, ku daina gardama a zancen gaskiya Mangoro dai nawa ne dan ni na tsinko shi daga kan bishiya". Haka dai suka rinka gardama da rants-rantse kan cewa ko wannen su na da'awar cewa Mangoro nasa ne.

Suna cikin wannan yamutsin sai ga Kare yazo wuce wa .Sai ya tsaya yana kallon hayaniya da tada jijiyoyin wuya da suke yi. Sai yace masu"wai kan me kuke wannan daga murya? Sai duk suka taho wajen sa , sai dayan su ya kada baki yace"Kare ka kasance mai hikima da kwarewa sakamakon zaman ka da mutane, saboda haka muna son kayi mana shari'a bisa adalci kan wanda yafi cancanta ya tafi da wannan Mangoro". Sai ko wannen su ya bashi labarin dalilin sa na cewa Mangoro nasa ne. Kare yayi tunani ,sai ya tambaya "wa ya fara ganin Mangoron ? Sai Zomo ya kada baki yace "ni ne! ni ne ! Sai kare ya sake tambaya "wa ya tsinko Mangoro? Sai Kurciya tayi tsalle ta ce "ni ce! ni ce na tsinko! Sai kare ya sake tambaya " wa ya dauki Mangoro bayan an tsinko? Sai Bushiya ya ce "ni ne! ni ne domin a baya na ya fado! Sai Kare ya yanke masu hukunci kan cewa "matsalar da kuke fuskanta shine ko wannan ku nada iko akan Mangoro, amma Mangoro guda daya ne , saboda haka na yanke hukuncin cewa za'a raba maku Mangoro ku daidai gida uku".

Mamaki da murna ya kama dabbobin gaba daya kan hukuncin da Kare ya yanke masu. A take Bushiya ya dauko Mangoro daga bayan sa ,ya raba gida hudu. Ya fara mika wa Zomo "ga rabon ka saboda fara ganin Mangoro". Sai ya mika wa kurciya yana cewa "ga naki rabon dan tsinko mangoron da kika yi". Sai ya baiwa kansa wani bangaren yace "saboda ya fado a baya na". Sannan ya baiwa Kare wani bangaren yace "ga naka " Kare yayi mamakin gaske cike da farin ciki sai ya ce "me yasa nima kuka bani wani bangaren a matsayin rabo na?" Sai Bushiya ya ce "saboda ka bamu shawaran da muka ji dadi ". Ta wannan hanyar dukkan su suka sami rabon shan Mangoro mai dadi cikin jin dadi da annashuwa.

Darasin da wannan labarin ke koyar wa ita ce raba dai dai aiki ne mai kyau domin yana kawo farin ciki da warware matsaloli da dama.

Haza wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Wednesday, 10 October 2007

ARE TRADITIONAL AND RELIGIOUS LEADERS IN SUPPORT OF THE MASSES?

By Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Among community leaders in Nigeria, the traditional and religious leaders do receive special respect from the people as they are regarded as fathers of the society. They are regarded as burning candles that show the way on how the society should live based on their forms of belief. Also it is their duty on commanding the community on performance of good deeds and forbidding them to commit what is unlawful.

Masses had a very special regards and respect for traditional and religious leaders as they believed that they would never support and encourage any issue that will harm their ways of life. But unfortunately, recently some of them have reversed and changed their attitude by becoming errand boys of those in power and moneybags. It is an open secret today that many of them have joined the club and convoy of the ruling class or always in total support of any government in power.

Clerics as religious leaders all over the world are known to be on the side of justice ,truth, equity and accountability, and they also preach to their followers to be on the side of truth and justice. They are steadfast as they are never afraid to say the truth and side with justice no matter how bitter it is. Also they never collaborate with oppressors, tyrants, looters and ungodly leaders. Religious history books are full of narrations of how God fearing clerics fought against injustice, tyranny and suppression. Some of them had even led their countries in the fight against uprooting tyrants, oppressors and stooges from power. They are actively involved in the fight against all forms of injustice and discrimination against their people and even in the forefront in the struggle for democratic governance.

Even during our present times we saw or heard of religious leaders that have led their people to defeat tyranny and oppression, and those that were persecuted and jailed or were forced to exile or even killed for saying and siding with the truth and justice by some few individuals who have control of the government machinery.

Today, before our own eyes, some Clerics have changed the meanings and interpretations of their Holy Books to suit the intrest of political leaders so that they could smile back to their banks. What is happening today is that if you force your way corruptly to power through massively rigged election, they will say God gave you the power! If you loot from the treasury they will say God has enriched you !! If you implement policies against the wishes of the people, they will say God said you should be followed!!! Also you will find these Clerics on their ways to government houses federal, state and local or in the homes of those that all knows how they amass their wealth.

Am not saying that it is an offence for traditional and religious leaders to relate with the political and ruling class, but what is happening always is that they don't inform the ruling class the real condition of the masses and the country. Masses are really suffering due to lack of infrastructures. But the traditional and religious leaders never speak up and always pretend as if everything is moving smoothly. Whenever they speak it is on the masses to always live peacefully and abide by the laws without speaking out to the ruling class to rule with justice and equity.

It can't be denied that traditional and religious leaders have special prestige in Nigeria. Is it that the prestige they have is not enough that they have to be errands of the political class? And are there any worldly materials they lacked that led them to be boot licker of the political class? Are they aware that masses can now dictate their personal intrest when they propagate it as religious injuctions? Are they of the opinion that being errand and cohorts for those in power is the only avenue to protect their seats and gain influence? And when will they seek respect for themselves as true leaders of the society and people stop calling them agents of whoever is in power?

Traditional and religious leaders are those leaders that the masses tend to have good opinion about as they provide guidance and protect their rights when the need arises. Is it not a betrayal that these leaders tend to be more concerned about their own personal interests? Don’t they think that the masses can have a very bad opinion about them?

The history of many countries of this world is full of roles played by Kings and the Clergy. Why is it that today in some parts of the world they tend to play little or no role in such countries today? The answer is clear as these leaders par take in the exploitation and tyranny against their own people and when change arrived those countries they were not spared. And that is the reason why in some countries there are no traces of traditional rulers and the religious leaders lose their prestige and power of commanding the good and forbidding evil.

Where are those traditional rulers that have supported election riggers into power? The history of our country is replete with how those helped to hold onto power illegitimately repay their benefactors? Also religious leaders that sided with the authority against the wish and aspirations of their people tend to lose respect and dignity as they are viewed as agents and cohorts of those in power.

Respect and prestige will be more for traditional and religious leaders if they side with the masses. And they should have the principle of advising the ruling class truthfully, and informing them of how life of the common man can be improved and stoppage of all government policies that are anti-people. And if they happen to visit government houses from federal to local government it should be for the intrest of the masses not to seek for contracts, royalties and political appointments for themselves and families. Also they should be bold enough to say the truth to the ruling class as they can say it to the masses. They should be in the forefront in any struggle to resist government policies that are unpopular such as increase in petroleum products but not the NLC!

God fearing and purposeful leadership is loved by people. Any leader that loots either before or now should not be seen associating with traditional and religious leaders as such association increases the continuation of corruption as future leaders can always think that if they loot and share the loot through building places or worship and obtaining traditional titles they will be respected and escape justice. Traditional and religious leaders should reciprocate to the masses the same way they hold them in esteem; anything short of this could lead to anarchy as it will be unfortunate if they call people to order and no one listens to them, then who will provide guidance to the society?

Saturday, 6 October 2007

Badakalar kwangila :Ya wajaba Etteh Tayi Murabus!

Mace ta farko da ta fara rike mukami mafi girma a Nigeria wato Uwargida Patricia Olubunmi Etteh na shugabantar majalisar wakilai na cikin tsaka mai wuya ko kuma ace tana cikin halin dana sani saboda halin da ta tsinci kanta na badakalar zargin aringizon kwangilar kwaskwarimar gidanta da mataimakinta Hon. Babangida Nguroje da motocin alfarma guda goma sha biyu kan tsabar kudi naira miliyan dari shida da ashirin da takwas!

Kamar yadda kwamitin Idoko ya bada rahoton sa ,sun sami shugabar majalisar da laifi dunu-dumu kan zargin da ake yi mata inda kwamitin ya gano cewa ba'a ma bi tsarin daya kamata ba wajen bada kwangilolin,domin da farko ba'a tallata kwangilar ba a jaridu ,na biyu kanfanonin dake kwangilar basu da rajista da hukuma da wasu laifufukan da kwamitin ya bankado.Amma ita Uwargida Etteh ta dage kan cewa bata da laifi saboda haka ba zata amsa kiraye-kirayen da ake tayi mata ba na tayi murabus ko ta fuskanci tsigewa.

Mafi yawan 'yan Nigeria nada ra'ayin cewa a wannan halin da talakawa ke cikin bakin talauci da fatara ace an sami shugabar majalisar wakilai ta kashe zunzurutun kudi na miliyoyin nairori har sama da dari shida saboda kwaskwarimar gidaje da sayen motocin alfarma bai dace ba.Sannan wasu na ganin cewa bata ma chancanci rike mukamin ba saboda rashin gogewa da ilimi mai zurfi,saboda sana'ar data goge a kanta itace na gyran gashi!Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ne ya dankara wa 'yan Nijeriya ita saboda dalilan dashi kansa yafi kowa sani.

Tun lokacin da wasu 'yan majalisar wakilai karkashin lemar "Integrity Group" bisa jagorancin Hon.Faruk Lawan da John Halims Agoda Da Mercy Almona Isei suka shiga gwagwarmayar ganin Etteh ta rabu da kujerar ta magoya bayan ta ke zargin su da cewa suna wannan kaiwa da komowa ne saboda basu sami biyan bukatun su ba na shugabantar kwamitocin majalisar masu maiko. Shi dai Hon.Faruk Lawan shine jagoran wadanda suka tsaya har Etteh ta kujerar shugabancin majalisar wakilai an kuma wayi gari a yau shine jagoran masu son ganin bayan ta !

Bankado badakalar aringizon kwangilolin gyran gigan su Uwargida Etteh ke da wuya harkokin majalisar wakilai ya tsaya chak.Rabon majalisar ta zauna domin tattauna da tsara dokoki an kwana biyu saboda Etteh na fargaban majalisa ta zauna dan bata san yadda za'a kwashe ba. Lallai Uwargida Etteh ta tafka abun kunya da Allah-wadai ,ta kuma zubar da mutunci da kimar majalisar tarayya a idanun 'yan Nijeriya saboda haka ya zama wajibi ,ya zamo tilas tayi murabus! In kuma taki to lallai ya wajaba ga 'yan majalisar wakilai su tasa keyar ta , ta hanyar tsigewa sannan hukumomin yaki da cin hanci da almundahana suyi aikin su a kanta.

In har da gaske gwamnatin Alhaji Umaru Musa 'Yar'adua keyi na da'awar yaki da cin hanci da rub da ciki da dukiyar al'umma to su shawarce ta tayi murabus domin tana rike da mukami mai muhimmancin gaske na tsara wa kasa dokoki.Sannan zai zama wata dama ga gwamnatin na 'Yar'adua su rabu da yan amshin shatar Obasanjo da suke nema suyi wa gwamnatin sa kene-kane.

Ya kuma kamata Uwargida Etteh ta amsa kiraye-kirayen da shugabanin siyasa da addini da al'umma keyi mata na tayi murabus .Wannan kiraye -kiraye da ake yi mata ya nuna cewa a fili bata da goyon bayan 'yan Nijeriya,Sannan inda wani mutunci ko martaba da suke anin ta dashi ,to ya zube.Ita kuma a kokarinta na ganin cewa bata sauka daga kujerar ta na shugabantar majalisar waklai ba ta dauki wasu matakai da zasu kara jefa ta cikin tsaka mai wuya.Domin da farko tayi amfani da kabilanci ,inda ta kaiwa Alhaji Lamidi Adedibu ziyara shi kuma yayi maganganun neman tada zaune tsaye inda ya dangata matsalar ta da makomar kabilar 'Yarbawa.Haka kuma taso tayi amfani da addini inda ta bada umarnin masallacin dake gidanta mazauni sannan ta gina majami'a.

Ya kamata ta san da cewa ba wai 'yan Nijeriya sun tsane ta bane dan kawai tana mace ko Bayarabiya ba a'a suna ganin cewa bukatun kanta da jin dadin ta kawai shine a gaban ta.Saboda labarai dake fitowa game da ita suna nunawa ne zuwa ga almubazaranci.Tayi bikin kece raini a ranar zagayowar ranar haihuwar ta a kasar Amurka,ga kuma neman da tayi a saya mata injin tausa na miliyoyin nairori! Ga kuma wannan badakalar na kwaskwariman gida, gaidan da kwanannan Alhaji Aminu Bello Masari ya fita a cikin sa bayan zama na shekaru hudu da yayi.

Uwargida Etteh ta baiwa 'yan Nijeriya musamman mata da kabilar ta na 'Yarbawa kunya.Domin kungiyoyin mata da suka yi ta tsalle-tsalle na murnan ganin cewa hakar su ta fara cimma ruwa na ganin cewa ana damawa dasu a kololuwar siyasar Nijeriya ta basu kunya domin ta aikata abinda mazan da suka jagoranci majalisar basu aikata ba.Ta bangaren kabilar ta na 'Yarbawa ta sake dama masu lissafi domin ya sake bayyana a gare su cewa halin bera da handama da babakere bai takaita ga wasu kabila ko yankin kasar ba a'a matsala ce dake tattare da rashin adalci da rikon amana da kishin kasa.

In 'yan majalisar wakilai suka yi nasarar kawar da Etteh ko kuma taga haza tayi murabus a kashin kanta,to ya kamata suyi kyakyawan nazari bisa mahangar adalci kan wanda zaifi dacewa ya ko ta jagoranci majalisar.Cikin abubuwan da zasu duba shine na zaben wanda ake ganin cewa baya fuskantar barazanar soke zaben sa saboda tafka magudin zabe a gaban kuliya manta sabo.Da kuma duba mutumin da suke ganin cewa ba zai zama karen farauta ko dan amshin shata ga "Aso Rock"ba.Irin shugaban da suka zabar ma kan su shine madubin da al'umma zasu yi ta kollon su dashi.Misali irin shugabancin da Aljaji Ghali Umar Na'abba yayi wa majalisar wakilai a zango na farko ya bata daraja da kwarjini a idon 'yan Nijeriya da kasashen waje.Haka ma shugabancin da Alhaji Aminu Bello Masari yayi wa majalisar shi ya bata ruhin da ta sami chajin murkushe tazarce.

Lokaci yayi da Uwargida Patricia Etteh zata amsa kiran yan Nijeriya tayi murabus.Kasantuwar ta da cigaba da jagorantar majalisar wakilai ba a bin amincewa bane ga 'yan Nijeriya saboda ta bayyana tana da laifi a badakalar kwangilolin kwaskwarimar gidanta dana mataimakin ta kamar yadda rahoton kwamitin Idoko ya bayyana.Mutunci madara ne in .....

Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Sunday, 30 September 2007

TUNAWA DA RANAR KUDUS: RANAR JADDADA GOYON BAYA GA PALASTINAWA

A watan Yuli na shekarar 1979 marigayi Imamu Ruhullah al-Khomeini(r.a)ya bada fatawa ga al'ummar Musulmin duniya da masoya 'yanci da adalci na cewa kowace ranar Jumma'a ta karshen watan Ramalana ta kasance ranar Kudus. Kuma wannan fatawar ita ta canza al-kiblar gwagwarmayar Kudus da Palastinawa daga gwagwarmayar yan kasanci da Larabawa zuwa wani al'amari da ya hau kan al'ummar Musulmin duniya.

Menene Ranar Kudus? Kudus ta kasance Palastinu ga al'ummar Musulmi,ga su kuma Yahudawa ta kasance kasar Isra'ila. A kasar Kudus Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas yake inda ya kasance al-Kibla ta farko ga Musulmi ,kuma Masallaci na uku mafi daraja bayan Ka'aba mai girma da Masallacin Manzo Muhammad(saw)dake garin Madinatun Munauwara.

Ranar Kudus ta kasance rana ta hadin kai a tsakanin Musulmin duniya domin tunkarar matsalar Kudus da ta kasance abunda ya shafi dukkan Musulmi,kuma ranar Kudus ta kasance ranar da Musulmin duniya zasu isar da sako da murya guda domin al'ummar duniya ta sani ko a sake tunatar da ita irin zaluncin da danniya da kama karya da cin mutumcin da Yahudawan kasar mamaya ta Isra'ila kewa al'ummar Palastinawa dama Musulmi musamman kasashen Musulmin dake makotaka da Isra'ila.Ranar Kudus ta kuma kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tattauna tare da nemo mafita game da halin da al'ummar Palastinu suka sami kan su da tono da bankado irin makirce-makircen da kasar mamaya ta Isra'ila kewa Palastinawa da al'ummar Musulmi a ko'ina cikin duniya.

Shekarun bayan yakin duniya na biyu zasu kasance a bin tunawa da jimami ba wai ga al'ummar Palastinu da Musulmi kadai ba ,a'a harma da masoya 'yanci da adalci da walwala a ko'ina cikin duniya saboda mamayar zalunci da mulkin mallaka na babakere da Isra'ila tayi wa Palastinu.Sannan labari ne sananne ta yadda kasar Isra'ila ta jera shekaru tana karkashe Palastinawa mata da yara da tsofaffi,tare da rusa masu gidaje da gonaki da makarantu da asibitoci da wuraren sana'a da tilastawa dubun dubatan Palastinawa hijira zuwa wasu kasashe .Duk da irin zaluncin keta da ta'asar da Isra'ila keta aikatawa har yanzu ,kasashen dake da'awar 'yanci da kare hakkin dan-adam da dimokaradiya ke tallafawa Isra'ila da bata cikakken kwarin gwiwa kan abinda take aikatawa na assha ga al'ummar Palastinu musamman kasar Amerika.

Ranar Kudus rana ce ta masoya yanci da adalci da zaman lafiya da daidaituwa da mutumta hakkin dan-adam a ko'ina cikin duniya wadanda suke nuna goyon bayan su ga Palastinawa da ake zalunta da kuma kokarin isar da sakon halin kakani-kayin da Palastinawa ke ciki ga wadanda basu sani ba ko kuma suka jahilci halin da Palastinawa e ciki a hannun kasar Isra'ila .Kuma ranar Kudus ta kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tunatar da kawunan su cewa Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas baya karkashin kulawar su da ikon su.Kazalika Ranar Kudus ta kasance ranar da kusan shekaru ashirin al'ummar Musulmi dake da wayewa ta siyasar duniya dama wadanda ba Musulmi ba da suka tsani zalunci da danniya ke isar da sakonni ta hanyoyin da yafi yi masu sauki na isar da sakon su na Allah -wadai ga kasar mamayar Isra'ila da nema wa Palastinawa da ake zaluntagoyon baya domin al'ummar duniya su tallafa masu.

Ranar Kudus ta kasance rana ta musamman saboda ta kasance ranar da ake sake jaddada goyon baya ga al'ummar Palastinawa wanda Musulmin duniya keyi harma da masoya 'yanci a ko'ina cikin duniya.Ranar Kudus rana ce ta sake samun natsuwa a zukatan Musulmin duniya da Palastinawa kan sanin cewa dole wata rana Kudus ta komo hannun Musulmi da Palastinawa.

Mu rika tunawa da Ranar Kudus ta hanyoyin da zamu iya koda kuwa yaya yake domin mu nuna wa al'ummar Palastinawa da ake zalunta cewa muna tare da su, su kuma kasar mamaya ta Isra'ila su san da cewa bama goyon bayan ta'assar da suke aikatawa sannan muna Allah-wadai da zaluncin da suke aikatawa.Sannan mu sake jaddada muhimmancin Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas ga Musulmin duniya.

Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

LET THE COURTS DECIDE YAR'ADUA'S LEGITIMACY

Delivering his speech after been sworn-in as President and Commander in chief,Alhaji Umaru Musa Yar'adua admitted that the election that saw to his position was flawed.Also the reports of both local and international observers and reactions of opposition parties clearly stated that the election was sub-standard and lacked the proper procedure of accepted election.

Opposition parties and candidates that contested under their platforms did the accepted form of protest,which is laying their grievences before the election tribunals rather than inciting their party members and supporters to take the law into their hands.By this,the opposition received applause as this action of theirs potrayed them as peaceful and law abiding ,and they also became vigilant,as some politicians want to take advantage of the situation to hold on to power.

Former President Olusegun Obasanjo and Chairman of INEC Prof. Maurice Iwu are of the opinion that the election is a job well done and on the other hand the reports of observers,who reported that the April elections was the worst ever in the whole world.It is only the courts that will decide who is the liar between them!

Events unfolding after the April elections with regards to the opposition parties are disheartening and shameful especially with regard to opposition ANPP. Firstly ,the party came out loud and clear during and after the April elections that the election was massively rigged ! And later they changed gear by accepting to par take in goverment of national unity eventhough they had filed a suit against the presidential election!! Lastly they withdrew their suit against the presidential election in total disregard to the yearnings and aspirations of their supporters who underwent untold sufferings and hardships in the name of national unity!!!

Also information available indicates that the opposition AC and it's presidential candidate Alhaji Atiku Abubakar had been under pressure to also withdraw their suit against the presidential election .Will they also succumb to pressure and change their position by withdrawing their suit against the presidential election?

Still on the issue of withdrawing the presidential suit from courts,the media featured the news of attempt to convince General Muhammadu Buhari to withdraw his suit against the PDP,Alhaji Umaru Musa Yar'adua and Dr. Goodluck Jonathan.The delegation was led by former President Alhaji Shehu Shagari ,Galadiman Katsina Justice Mamman Nasir,Chairman First Bank Alhaji Umaru Mutallab and former chairman of defunct Democratic party of Nigeria (DPN)Alhaji Saleh Hassan,where they discuss extensively with General Buhari on the need for him to withdraw his suit in the electoral tribunal in the intrest of Northern and National unity.On the part of General Buhari he informred them on his determination to continue with his suit in the election tribunals.

Am of the opinion that pressure ,threat and intimidation should not be used on opposition parties and their flagbearers to to withdraw their suits in the election tribunals.,as it would not augur and speak well of our democracy .It is a must on us Nigerians to show the world our determination and sincerity in the process of building a sound and durable democracy in our country eventhough some individuals did what they did during the April elections.Nigerian policicians never learn from history and as such let us allow the courts to do their jobs as verdicts passed will serve as deterrant to future elections.Up coming politicians will also learn the process of how to legitimately become leaders and representatives of their people.

To President Umaru Musa Yar'adua, if those parading themselves as negotiators for pressuring ,intimidating and threatening the opposition parties and their flagbearers to withdraw their suits in courts are doing on your behalf ,Sir, you should stop them ,as it would send a bad signal to Nigerians and International community that your reforms on the electoral process are nor sincere.And Mr.President ,why are you afraid?There seems to be only two options now left which are either the courts to legitimise your election or to nullify the election.If Nigerians are satisfied with the way you conduct the affairs of this nation in the few months you ruled ,they will massively vote for you!

The massively rigged April elections and suits in election tribunals superceded the issue of Northerness,tribalism,religious sentiment and sectionalism.It is an issue of justice and providing exempleanery history for unborn Nigerians .It is also a must for us as Nigerians to ensure that process of assuming the mantle of leadership is constitionally followed for enshrinement of justice ,unity and purposeful leadership.

Eventhough many Nigerians are of the view that in the few months that President Yar'adua ruled Nigeria he has been able to achieve alot in such a short period,among his achievements are availability of fuel in all filling stations nationwide at a uniform price,revoking the sales of Kaduna and Port-Harcourt refineries,revoking of so many contracts that were not properlyawarded by the previous Obasanjo administration,stopping the mass sacking of the Nigerian workers and even returning many to their duty post e.t.c. With so many achievements in few months ,it still did'nt stop many from within and outside the country to continue to regard his goverment as illigitamate! President Yar'adua can only legitimise his goverment through the courts.All those seeking the opposition parties and their flagbearers to withdraw their suits from courts are not sincere advisers to President Yar'adua! It is only the final verdict of the courts that can place Yar'adua's goverment in it's proper position.

General Buhari has today remained the only true democrat standing! He should be aware that the struggle he is into of strenthening our democracy and the rule of law is appreciated and suported by all true lovers of democracy .And Buhari has reached a special stage where he has now occupied an exalted seat in the hall of fame of true democrats ,not only in Nigeria but in Africa as a whole.General Buhari should continue with his case in the election tribunal up to the supreme court without succumbing to pressure,threat,intimidation and blackmail ,as his suit is on behalf of the Nigerian masses.

Opposition parties that have joined the goverment of National unity and those that have withdrawn their suit in the presidential election had deceived and betrayed their members and supporters.They should be aware that history has prepared for them a special place and their parties may meet the fate of AD !

Nigerian masses should resist any attempt to turn their country to a one-party state,and should not be tired in any way in the struggle to place Nigeria among the nations where free and fair elections could be obtained.A new Nigeria that all will be proud of especially the black race all over the world.

Politicians in all political parties that have filed suits in the election tribunals should continue pursuing their cases and that of their supporters uptill the supreme court.It is a collective must on all Nigerians to ensure that our country earns respect and prestige in the world political arena.


Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Tuesday, 18 September 2007

A BAR KOTUNA SU HALASTA ZABEN YAR'ADUA

A jawabin da Alhaji Umaru Musa Yar'adua yayi bayan rantsar da shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya ya fito karara ya amince da cewa an sami kura-kurai a zaben daya kaishi ga zama shugaban kasa .Sannan kuma rahoton kungiyoyin sa-ido da martanin da jam'iyyun adawa suka bayar bayan zaben na watan afrilu na nuni da cewa basu gamsu da zabubbukan ba.

Jam'iyyun adawa da yan takara a karkashin jam'iyyun nasu sun yi abinda ya dace , wato maimakon yanke wa kansu hukunci ta hanyar tunzura magoya bayan su , su tada zaune tsaye sai suka shigar da kararaki a gaban kotunan zabe dan neman abi masu kadin hakkin su dana magoya bayan su .Kuma wannan mataki da suka dauka ya janyo masu yabo da sam barka domin ya nuna cewa suna son zaman lafiya da kishin kasar su da toshe duk watav kofa da wasu zasu cimma burin su na siyasa.

Duk da ikirarin da tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta (INEC)Farfesa Maurice Iwu keyi na cewa zabe sam barka da kuma rahoton kungiyoyin sa-ido dasu kuma suka bada bayanan cewa ba'a taba zabe mai muni ba a duniya kamar zaben Nijeriya na wannan shekarar.To ko a nan akwai bukatar kotu ta fayyace mana tsakanin su , su wanene makaryata!

Abubuwan dake ta faruwa a kasar nan tun bayan zabe ta bangaren jam'iyyun adawa nada ban takaici musamman ta bangaren jam'iyyar adawa ta ANPP. Da farko suka fito sukayi babatun cewa an atafka magudi suka dawo suka karbi goron gayyata na shiga gwamnatin hadin kan kasa duk da cewa sun shigar da kara a gaban kotu .Sai gashi sun janye karar da suka shigar a kotu kan zaben shugaban kasa ba tare da duba irin halin matsi da takura da magoya bayan su suka shiga ba da sunan cewa dan kasa ta zauna lafiya.Haka ma bayanai nata zuwa na cewa jam'iyyar AC da dan takarar shugaban kasar ta Alhaji Atiku Abubakar na fuskantar matsin lamba kan cewa suma su janye karar da suka shigar kotu.Ko suma zasu yi amai su lashe ?

Kan dai batun janye kararaki a gaban kotunan zabe ,kafofin watsa labarai sun ruwaito yunkurin shawo kan Janar Muhammadu Buhari ya janye karar sa dake gaban kotu kan batun magudin zabe da ya gurfanar da jam'iyyar PDP da Alhaji Umaru Musa Yar'adua da Dakta Jonatan Goodluck .Inda bisa jagorancin tsohon shugaban kasa Alhaji Shehu Shagari da Galadiman Katsina mai sharia Mamman Nasir da shugaban bankin First Bank Alhaji Umaru Mutallab da kuma tsohon shugaban rusheshiyar jam'iyyar DPN Alhaji Saleh Hassan suka yi zama na musamman da Janar Buhari domin shawo kan sa ya janye karar sa dake gaban kotu ,saboda suna ganin cewa ta haka za'a sami hadin kai da zaman lafiya a kasa.Ta bangaren Janar Buhari bai yi kasa a gwiwa ba wajen sanar dasu cewa zai cigaba da bin kadin shari'ar sa.

Ni a ganinav bai kamata ana tursasawa jam'iyyun adawa da yan takara su janye karar da suka shigar kotu ba.Yin haka tawaya ne ga tsarin dimokaradiya .Dole ne mu nuna wa kasashen duniya cewa da gaske muke bisa da'awar bin tsarin dimokaradiya duk da abinda wasu suka aikata a lokacin zaben wannan shekarar.Yan siyasar Nijeriya basa daukan darasi da yiwa kansu fada,amma in shari'a tayi aikin ta ,to zai zama darasi ga yan baya gun ganin cewa sun bi hanyoyin da suka dace dan zama shugabanni da wakilan al'umma.

Ina kuma kira ga shugaban kasa Alhaji Umaru Musa Yar'adua , da in da bazar sa ake rawa wajen kokarin ganin cewa an shawo kan yan adawa su janye kararakin su dake gaban kotu ,to lallai ya tsawatar ya kuma hana saboda zai nuna cewa bada gaske yake ba kan gyara batun zabe da kuma kokarin sa na tsabtace harkokin zabe. Kuma tsoron me yake ji ! Cikin biyu dole a yi abu guda wato ko kotuna su tabbatar da zaben sa ko kuma su rushe zaben suce a sake ,in yan Nijeriya sun gamsu da ayyukan da yayi a watannin da suka gabata sai su zabe shi !

Zancen magudin zabe da kararakin dake gaban kotuna sun shige zancen Arewaci ko Kabilanci ko Bangaranci ! Zance ake kan tabbatar da adalci da samar da kyakyawar turba a tarihi yayin da yan baya zasu karanci tarihin kasar nan anan gaba Dole ne a dawo da tsarin samar da shugabanci bisa turban gaskiya da adalci da rikon amana.

Duk da cewa wasu yan Nijeriya na ganin cewa Shugaba Yar'adua yayi rawan gani a wasu fannonin a watannin da yayi bisa kujerar mulki kamar samar da wadatattcen man fetur a farashi bai daya da soke cinikin matatar man fetur na Kaduna da Fatakwal da wasu kwangilolin da basa bisa ka'ida a gwamnatin baya da dakatar da korar ma'aikata dama dawo da wasun su bakin aiki da sauran su. Duk wannan bai hana wasu a cikin gida da kasashen waje daina ganin gwamnatin sa a matsayin haramtacciyar gwamnati ba! Shugaba Yar'adua na iya samar wa gwamnatin sa halacci ne kadai ta hanyar kotuna!! Masu kaiwa da komowa domin ganin an janye kararakin ba masoya na gaskiya bane ga shugaba Yar'adua!!! Gaba tafi baya yawa dan tarihi ba zai kyale duk wanda dashi aka dafa aka sha a zaben wannan shekarar ba sai in har kotu ta zartar da hukuncin ta.

Janar Buhari a yau ya kasance gwarzon dimokaradiya shi kadai tilo,ya san da cewa gwagwarmayar da yake yi na gyara al'amurran dimokaradiyya a Nijeriya a yau duk masoya cigaban dimokaradiyya na gaskiya na tare da shi .Kuma ya san da cewa ya taka matsayi na musamman a farfajiyar bunkasar dimokaradiya ba'a Nijeriya kadai ba a'a a Afrika gabaki daya.Kada ya ja da baya ya bi kadin shari'ar da ya shigar a madadin talakawan Nijeriya har kotun koli ta kasa!

Jam'iyyun adawa da suka shiga gwamnati da wadanda suka janye shari'ar da suka shigar kotu su san da cewa sun ci amanar yan jam'iyyar su da magoya bayan su.Su kuma sani cewa lallai tarihi ya tanadar masu inda zai ajiye su,kuma tabbas su saurari makoma irin ta jam'iyyar AD!

Ga talakawan Nijeriya kada mu taba yarda a maida kasar mu mai bin tsarin jam'iyya guda, kuma kada mu gaji da gwagwarmayar sai kasar mu ta shiga sahun kasashen da ake zabe na gaskiya da amana ,kasar mu ta kasance abun koyi ga kasashen Afrika da abin alfahari ga bakaken fata a ko'ina cikin duniya.

Yan siyasa a kowane jam'iyya da suka shigar da kara a kotu su cigaba da bin kadin hakkokin magoya bayan su har kotun koli.Dole ne mu hada karfi da karfe wajen dawo da martaba da mutumcin kasar mu a idon kasashen duniya.

Haza wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Thursday, 5 July 2007

KO YA DACE JAM’IYYUN ADAWA SU SHIGA GWAMNATIN HADIN KAN KASA?

Tun ranar da aka rantsar da Alhaji Umaru Musa Yar’adua a matsayin Shugaban Kasa ya amince da cewa an sami kurakurai a zaben daya kaishi kan kujerar shugaban kasa.Ya kuma nuna sha’awar hada kai da yan’adawa domin ciyar da kasa gaba. Da wannan tayin yan’adawa ke ta kaiwa da komowa kan amincewa ko a’a da gayyatar da Shugaba Yar’adua yayi masu har dai suka amince suka karbi goron gayyata.
Wannan tayin da alamun zai kawo rarrabuwan kai tsakanin yan ‘adawa saboda har an sami sabanin ra’ayuka tsakanin yan’takarar shugaban kasa a jam’iyyun adawa manya wato jam’iyyun ANPP da AC. Jam’iyyar ANPP ce ta fara amsar goron gayyatar, yayin da dan takarar ta na shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari yaki amincewa saboda a cewar sa suna gaban kotu kan rashin amincewar su da sakamakon zaben .Ta bangaren jam’iyyar AC sun bayyana sharadan da in aka amince dasu to zasu amsa goron gayyata ,inda daga bisani da dan takarar ta na shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya dawo gida Nijeriya daga neman magani a kasashen waje ya bayyana matsayin sa na cewa ba zasu amshi ko shiga gwamnatin Yar’adua ba saboda suna gaban kotu.
Da alamun shugaba Yar’adua yayi babban nasara wajen dakushe kaifin yan’adawa saboda an sami banbancin matsaya tsakanin manyan jam’iyyun adawa da yan takarar shugaban kasa a jam’iyyun su .Jam’iyyun na ganin cewa tunda shugaba Yar’adua ya name su kan warware matsalolin da suke addaban Nijeriya to ya zama wajibi su zauna su tattauna domin samin mafita.Su kuma yan’ takarar shugaban kasa a jam’iyyun na ganin cewa tunda suna gaban manta sabo kan ki da amincewar da zaben gaba daya to babu dalilin da zai sa su zauna teburi guda da Yar’adua a matsayin Shugaban Kasa sai in har kotu ta zartar da hukuncin ta.Wannan sabanin ra’ayin na Buhari da Atiku da jam’iyyun su na iya janyo dangantaka mai tsami ko raba gari gabaki daya a tsakanin su.
Shugaba Yar’adua na neman goyon bayan yan’adawa ne duk da yanda daga farko shugaban jam’iyyar sa ta PDP Sanata Ahmadu Ali ya bayyana cewa babu bukatar shigowa da yan’adawa cikin gwamnatin PDP.Amma ganin cewa Shugaba Yar’adua ya kafe kan tafiya tare da yan ‘adawa, jam’iyyar sa ta PDP ta mika wuya.Cikin bukatun abubuwan da yake so su tattauna da yan ‘adawa sun hada da samo hanyar bunkasar tattalin arzikin kasa da warware matsalar yankin Neja Dalta da batun tsaron kasa da sake fasalin kundin tsarin mulkin kasa da kuma kawo gyara a tsarin gudanar da zabe .An kuma ruwaito cewa zai basu kujerun ministoci da jakadu da mashawarta dau wasu mukaman.
An fara zaman farko tsakanin Shugaba Yar’adua da jam’iyyun adawa ranar 26 ga watan Mayu .Cif John Oyegun da Sanata Ahmed Sani Yarima da Sanata Umar Kumo ne suka jagoranci tawagar jam’iyyar ANPP yayin da Cif Audu Ogbeh da Dakta Abubakar Rimi da Alhaji Bashir Dalhatu suka jagoranci tawagar jam’iyyar AC zuwa wajen taron.Inda Mataimakin Shugaban Kasa Dakta Jonatan Goodluck ya shugabanci taron a madadin Shugaban Kasa.Ya kumata mika nasu bukatun ga yan’adawa ,suka kuma yan’adawa suka mika nasu bukatun ga gwamnatin Yar’adua.Inda daga bisani jam’iyyar ANPP ce ta fara amincewa da hada kai da gwamnatin Yar’adua,sai kuma jam’iyyar PPA ,amma jam’iyyar AC na ta kwamgaba gwambaya saboda wasu na so wasu kuma suna tare da ra’ayin Alhaji Atiku Abubakar.
Amma me yasa manyan jam’iyyun adawa suka mika wuya ta hanyar amsar gayyatar shiga gwamnatin hadin kai? Wasu masu fashin bakin siyasa na ganin cewa jam’iyyun na adawa na ganin haka shi yafi dacewa a gare su saboda da alamun cewa gwamnatin Yar’adua ta zauna da gidin ta saboda sunyi kira ga al’ummar kasa da su fito zanga-zangar kin amincewa da gwamnatin Yar’adua a ranar 1 ga watan Mayu amma talakawan kasa basu amsa kiran nasu ba.Sannan kasashen duniyar duk da kiran yan ‘adawa na su kaurace wa gwamnatin Yar’adua sunyi watsi da kiran sun rungumi gwamnatin Yar’adua harma da gayyatar sa taron manyan kasashen duniya na G-8.Haka kuma suma jam’iyyun ‘adawa a jihohin da suka kafa gwamnati jam’iyyar PDP a jihohin sun gurfanar dasu a kotu kan zargin tafka magudi suma inda yanda guguwar canji dake bugawa a bangaren shari’a na iya raba gwamnonin su da kujerun su.Wasu kuma yan’adawar ba zasu iya zama shekaru hudu ba suna adawa saboda sunfi ganewa a dama dasu.Sannan akwai wasu cikin yan adawar da zasu mika wuya ga gwamnatin Yar’adua saboda suma a manta da yanda suka gudanar da mulkin jihohin su.Shugabanin al’umma daga Arewa suma sun kasance cikin sahun gaba na a baiwa gwamnatin Yar’adua cikakken goyon baya.Kungiyar ACF da NU duk sun rungumi Shugaba Yar’adua ,shima Sarkin Musulmi Saad Abubakar ya jagoranci tawagar sarakuna domin yiwa Shugaba Yar’adua mubaya’a, kazalika manyan malaman addini na Musulmi da Kirista duk suna yiwa Shugaba Yar’adua mubaya’a da kungiyoyi daban daban na matasa da yan’kasuwa da sauran su sun je sunyi wa Shugaba Yar’adua mubaya’a .
Janar Muhammadu Buhari na fuskantar babbar kalubale a rayuwar sa ta siyasa saboda in ya nace kan cigaba da bin kadin shari’rar sa a kotu sabanin matsayin jam’iyyar sa ta ANPP to zai iya kaiwa jam’iyyar ta dauki mataki a kan sa. Abokanen adawar sa a jam’iyyar AC na iya komawa inda suka fito wato jam’iyyar PDP saboda jam’iyyar har ta kafa kwamitin da zai dawo da ya’yan ta da aka sami sabanin ra’ayi suka bar jam’iyyar da su dawo a cigaba da harkoki dasu a jam’iyyar PDP.In haka ya kasance to Janar Buhari Kadai za’a bari kan shari’a da gwamnatin Shugaba Yar’adua.Amma bayanan dake fitowa daga offishin kamfen din tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar na nuni da cewa zai bi kadin shari’ar da ya shigar gaban kotu.Kuma wasu na ganin cewa dawowar tsohon Shugaban Kasa Obasanjo cikin harkokin jam’iyyar PDP a matsayin shugaban kwamitin dattawa na iya zama dalili na duk wadanda suke da matsala da Obasanjo suki amincewa da batun sulhun dawowar su jam’iyyar.
Wasu jam’iyyun adawa karkashin lemar NUD su kuma sun tubure kan batun kafa gwamnatin wucin gadi,wato suna kan bakan su na cewa Shugaba Yar’adua yayi murabus ya mika mulki ga gwamnatin hadaka ta wucin gadi domin gudanar da sabon zabe.Amma da wuya su iya wani tasiri saboda manyan jam’iyyun adawa guda uku wato ANPP da Ac Da PPA sun nuna sha’awar su ga samar wa Nijeriya mafita sabanin bin hanyoyin da baza su cimma wata nasara ba a tunanin su.
Wasu yan ‘Nijeriya na ganin cewa akwai bukatar yiwa Shugaba Yar’adua uzuri domin ayyukan sa na nuni da cewa da gaske yake wajen samun bakin zaren matsalolin da suka hana Nijeriya cigaba .Suna kuma ganin cewa ya dauki matakan da suka fara nuna cewa shi ba dan amshin shatar tsohon shugaban kasa Obasanjo bane.Suna kawo misalai da yanda ya amshi bukatun kungiyar kwadago harma da daukan alkawarin cewa gwamnatin sa ba zata kara kudin man fetur ba har nan da watanni goma sha biyu da kuma sakin Alhaji Mujahid Asari Dokubo da soke kwangilolin da tsuhuwar gwamnati ta bayar da basu cikin kasafin kudin bana .Ga kuma kira da yake tayi na kowa da kowa yazo ya bada gudunmawarsa ga cigaban Nijeriya.
In da gaske ake kan batun cigaban dimokaradiyya a Nijeriya to babu bukatar jam’iyyun adawa su shiga gwamnatin hadin kan kasa saboda haka na nuni ga kasantuwar Nijeriya mai jam’iyya guda daya .Adawa a dimokaradiyya dole ne! Kuma wannan hadin kan kasa za’ayi yayin da jam’iyyar PDP na da kasa biyu bisa uku a majalisun tarrayya da na dattijai ga jihohi har guda ashirin da bakwai!! Sai dai in jam’iyyun adawa zasu ci amanar magoya bayan ta ne !!! Wadanda aka kashe,aka daure ,aka ci zarafin su ya zama a banza kenan.Kuma a gaskiya jam’iyyun zasu shiga halin da jam’iyyar AD ta sami kanta a yanzu.Dole a yabawa Janar Buhar da Alhaji Atiku Abukakar kan tsahin daka da suke nunawa na ganin cigaban dimokaradiya a Nijeriya ,kuma su sani cewa dukkan masu son cigaban tsarin dimokaradiya ta gaskiya na tare dasu.Su kuma tsaya kan matakin da suka dauka babu gudu babu ja da baya.
Talakawan Nijeriya na kallon yanda al’amurra ke gudana da kuma fatan cewa kowa zai girbi abinda ya shuka ,saboda yan’siyasa da yan’boko a kasar nan bukatun kan su ne a gaba.Sannan suna zuba ido su gan yanda zata kare a gaban shari’a tsakanin gwamnatin Yar’adua da yan takarar shugaban kasa wato Buhari da Atiku domin da alamun jam’iyyun su zasu janye jikin su daga cigaba da bin kadin magoya bayan su a gaban kotu.
Haza Wassalam
Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com