Sunday, 10 February 2008

Obasanjo: Ruwa na neman karewa wa dan kada!

Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo a yan kwanakin nan na fuskantar tonon silili da suka iri-iri, tare da kiran da ake tayi na a bincike shi kan yadda ya tafi da kasar a shekaru takwas da yayi yana mulki . Ya kuma kasance tsohon shugaban kasa mafi bakin jini saboda yanda babu kakkautawa ya rika gallazawa yan Nijeriya har zuwa karshen mulkin sa inda ya kara kudin man fetur da haraji bayan shugabantar zabe mafi muni a tarihin zabubbuka a duniya.

Cikin wadanda babu zato babu tsammani suka soki yanda Cif Obasanjo ya tafi da kasar shine mutumin da yaci gajiyar magudin zaben da Obasabjo ya tafka , wato Shugaban Kasa Umaru Musa Yar'adua. Ya zargi gwamnatin Obasanjo da barnata kudi dala biliyan goma kan wutar lantarki amma babu wutar! Koda yake shugaban majalisar wakilai Dimeji Bankole yace kudin dala biliyan sha-shida ne! Haka nan a kullum sai tono abubuwan son zuciya da Obasanjo yayi ake tayi , kamar baiwa kansa lasisin mallakar gidajen rediyo da talebijin da yayi ana sauran yan'kwanaki ya bar mulki. Da gano wasu asusun boye har guda goma sha shida da biliyoyin nairori a dankare.

Mafi muni cikin abubuwan dake ta faruwa game da Obasanjo bayan ya bar mulki shine na zargin da dan'sa na cikin sa Gbenga Obasanjo yake yiwa mahaifin sa cewa yana lalata da matar sa yana bata kwangiloli. Gashi kuma babbar yar'sa Sanata Iyabo Obasanjo-Bello ita ma ana zargin ta da laifin damfara , inda ake zargin cewa ta damfari wani kamfanin kasar Austria mai suna M.Scheider GMBH &Co kudi har naira biliyan uku da rabi ,inda tayi amfani da sunan Uwargida Damilola Akinlawon.

Kafin Cif Obasanjo ya dawo bisa karagar mulki a shekarar 1999,yana cikin mutanen da ake gani da girma da kima a nahiyar Afrika da kasashen duniya.Ya kuma sami girman ne saboda yanda ya mika wa farin hula mulki a shekarar 1979. Sai aka wayi gari Obasanjo ya zubar da mutumcin sa da girman sa a cikin gida Nijeriya da kasashen duniya tun lokacin daya tafka magudin zabe a shekarar 2003, Sannan yaso a canza kundin tsarin mulkin kasan nan domin ya sami wa'adi karo na uku. Yan kasa masu kishi suka tarwatsa mumunan burin na Obasanjo na kasancewa a bisa mulki har mutuwan sa. Abunda ya faru bai ishe shi ishara ba , yayi wani yunkuri na wanke sunan sa , sai gashi bisa taimakon Farfesa Maurice Iwu sun gudanar da zaben da su uku kadai suka yi imanin an gudanar da zabe na gaskiya wato shi kansa Cif Obasanjo da Farfesa Maurice Iwu da Malam Buhari Daure !

A lokacin mulkin Obasanjo yayi ta sayar da kaddarori da kamfanoni da masana'antun gwamnati da zimmar bunkasa yanda suke tafi da al'amurran su, amma sai aka wayi gari yan kasa na zargin cewa an saida wadannan kayayyakin na kasa bisa farashin da bai kai darajar su ba. Sai kuma gashi a kwananan ana neman naira biliyan 146 na kudaden domin basu shiga asusun tarayya na kasa ba. Kazalika majalisar tarayya ta soke wasu daga cikin cinikayyan saboda basa bisa doka.

Yan Nijeriya da dama nata fitowa suna kira ga gwamnatin Umaru Yar'adua data binciki yanda tsohon shugaban kasa Cif Obasanjo ya tafi da kasar nan a shekaru takwas da yayi yana mulki.Kungiyoyi kamar su Afenifere da kungiyar Kiristoci ta kasa da kungiyar hadin gwiwan jam'iyyun adawa da manyan yan siyasa da talakawan kasa nata kira kan lallai Obasanjo nada bayanen da zaiyi wa yan kasa bisa zargin da ake tayi masa na halin fataken dare.

Ko a jam'iyyar sa ta PDP inda yake rike da kujerar shugaban kwamitin amintattu na jam'iyyar wato BOT,yana fama da suka da adawa inda wasu manyan yan jam'iyyar ta PDP ke neman yayi murabus. Cif Solomon Lar da Alhaji Abubakar Rimi na ganin cewa zargin abin kunya na lalata da matan dan'sa kadai ya isa hujja Obasanjo yayi murabus. Shi kuma tsohon shugaban majalisar dattijai Sanata Ken Nnamani na ganin cewa kujerar da Obasanjo ke kai na shugaban kwamitin amintattu kujerace ta Arewacin Nijeriya. Sannan shi da tawagar sa ta G21 na neman jam'iyyar ta koma kan kundin tsarin mulkin ta na shekarar 1998, wato a fakaice suna son a datse fukafukan Obasanjo a jam'iyyar .

Kuma da lamu yan siyasar Nijeriya na neman maida Obasanjo saniyar ware domin a yau duk tonon sililin da Obasanjo ke fuskanta daga cikin gidan sa zuwa kasa gabaki daya babu mai fitowa ya kare shi. Yau yan gani kashenin Obasanjo irin su Sanata Nasiru Mantu da Malam Nasiru el-Rufa'i da Cif Femi-Fani Kayode da Malam Nuhu Ribadu da Gwamna Sule Lamido da sauran su , babu wanda ya fito dan kare mutumci da martaban Obasanjo kamar yadda aka san su a baya suna yi.

Sannan Obasanjo ya zama saniyar ware a siyasar kasashen duniya da nahiyar Afrika saboda yanda ya gudanar da zaben 2007 a Nijeriya. A yau Mista Kofi Annan duk da cewa bai taba zama shugaban kasa a wata kasa ta Afrika ba ,bayan Mista Nelson Mandela babu wani dan nahiyar Afrika mai martaba da kiman sa domin ko rikicin magudin zabe dake faruwa a kasar Kenya shi ke kaiwa da komowa dan samin zaman lafiya a kasar.Girma da martaban da Obasanjo zai samu a Afika da duniya da suna dayawa daya kare mutumcin sa , amma sai gashi yayi karkon kifi daga shahararre a siyasar duniya da Afrika zuwa almajirin Lamidi Adedibu a fagen siyasa da siyasar yankin yarbaawa.

Yau kusan shekara guda kenn da Umaru Yar'adua yake bisa mulki amma ga dukkan alamu yanda Obasanjo ya kudundune kasar ya mika masa ya kasa gano zaren matsalolin dake damun kasar .Har yau babu wani cigaba da aka samu daya wuce soke ko kuma aiwatar da wasu manufofin gwamnatin Obasanjo. Rashin aikin yi da talauci da rashin tsaro da hauhawan farashin kayayyaki da sauran su sai karuwa suke tayi inda rayuwan talaka sai kara munana yake tayi.

Ko Shugaba Yar'adua zai amsa kiraye-kirayen da ake tayi masa na binciken gwamnatin Obasanjo? Haka ma suma majalisun tarayya shin zasu iya tuhuman Cif Obasanjo kamar yadda suke ta tada kuran zasu yi?Hadin gwiwan jam'iyyun adawa shin zasu iya tursasa gwamnatin Yar'adua ta binciki Obasanjo?

Ta bangaren yan Nijeriya suna da bukatar sanin yanda aka gudanar da dukiyar su a lokacin mulkin Obasanjo. Suna fatan cewa Shugaba Yar'adua zai nuna wa duniya cewa shi ba dan amshin shatar Cif Obasanjo bane ta hanyar kafa kwamitin bincike kan yadda Obasanjo ya tafi da arzikin kasar nan, in kuma aka same shi da laifi to lallai a hukumta shi,yin haka zai sa jama'ar kasa suyi ma Yar'adua kyakyawan zato. Tsakani Obasanjo da yan Nijeriya sai muce rana dai bata karya sai dai uwar ya taji kunya.


Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Tuesday, 1 January 2008

Zaben Kasar Kenya: Wani Koma Baya ga Tsarin Dimokaradiya a Afrika

Zaben da aka gudanar a kasar Kenya ranar 27 ga watan Disambar 2007 ya bar baya da kura da tambayoyi da dama kan cewa shin kasashen Afrika a shirke suke subi sahun kasashen duniya wajen gudanar da zabe na gaskiya da gujewa magudin zabe wajen baiwa talakawan su abinda suka zaba?Hukumar zaben kasar ta Kenya ta bayyana cewa Shugaba Mwai Kibaki ne ya lashe zaben sabanin harsashen farko dake nuni ga Mista Raila Odinga na kan hanyar lashe zaben.

Kasar Kenya ta kasance kasa mafi karfin tattalin arzikin a gabashin Afrika,kuma arzikin ta ya dauru ne akan yan yawon bude ido,inda kasar ke samun kudin shiga na miliyoyin daloli a kowane shekara.Zargin da jama'ar kasar keyi na an basu shugaban da basu suka zaba ba ya jefa kasar cikin tashe-tashe hankulan da daruruwan mutane suka rasarayukan su.

Kamar mafi yawan kasashen Afrika da kabilanci ke taka muhimmiyar rawa wajen cigaba da danne talakawa da tauye cigaba,inda shugabanni ke shigewa cikin rigar kabilanci su cigaba da mulki,kasar Kenya ta sami kanta a cikin wannan matsalar .Shugaban kasa mai ci Mwai Kibaki ya fito ne daga kabilar Kikuyu(mafi rijaye a kasar),inda shi kuma jagoran yan'adawa Raila Odinga dan kabilar Lous ne. Adawa da sakamakon zaben ya juye zuwa fadan
kabilanci tsakanin yan kabilun biyu.

Jagoran yan adawa Raila Odinga wanda jam'iyyun adawa karkashin lemar Orange Democratic Movement (ODM) suka tsayar shahararen dan siyasa ne a kasar kuma da'ne ga tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Jaramogi Oginga Odinga.Ya kuma fara takarar shugaban kasane a shekarar 1997 inda yazo na uku lokacin tsohon shugaban kasa Daniel Arap Moi wanda shi ya lashe zaben sannan shugaban kasar na yanzu Mwai Kibaki yazo na biyu. Odinga dan siyasa ne da yake da gagarumin goyon bayan talakawan kasar ,kuma yana da kyakyawan tsarin gudanarwa wajen iya cin zabe.An kuma ganin sa a matsayin dan siyasa dake da yawan canza sheka.

Shugaba Mwai Kibaki wanda yayi saurin rantsar da kansa awa guda bayan fadin sakamakon zaben ya aiwatar da ayyukan cigaba musamman ta fannin tattalin arziki inda arzikin kasar ya bunkasa. Kibaki ya karbi mulkin kasar bayan shekaru masu yawa da kasar ta kasance karkashin mulkin jam'iyya daya tilo wato Kenya African National Union(KANU). Shugabanni biyu ne suka shugabanci kasar ta Kenya bayan samun mulkinkai daga kasar Birtaniya a shekarar 1963 wato tsakanin Shugaba Jomo Kenyatta da Daniel Arap Moi kafin shekarar a shekarar 2002 Shugaba Mwai Kibaki ya jagoranci jam'iyyun adawa suka kada jam'iyyar KANU a zaben da aka gudanar a shekarar.

Zaben na kasar Kenya na fuskantar suka daga cikin kasar da wajen kasar .Kungiyoyin sa ido sun shaida cewa an tafka magudi a zaben.Kuma wani abinda ke karfafa wa yan'adawar kasar gwiwa shine na cewa kuri'o 230,000 kawai ne rata tsakanin Kibaki da Odinga kuma jam'iyyar Odinga ita ta lashe mafi yawan kujerun majalisun kasar ,wannan shi yasa suke zargin cewa da anyi kidayan gaskiya da sun lashe zaben da gagarumin rijaye.Ko kungiyar sa ido na tarrayyar Turai sun shedi cewa anyi aringizon kuri'o saboda a cewar shugaban nasu Mista Alexander Graf Lambsdorff , yace "an hana mu shiga wuraren da ake tattara tare da kidaya kuri;o kuma sakamakon da hukumar zaben kasar ke bayar wa ya sha ban-ban da sakamakon dake fitowa daga inda akayi zabubbukan".

Abubuwan da suka faru a kasar Kenya bayan zaben abin takaici ne da kunya ga kasar Kenya .Kamar Nijeriya , itama ta kasa gudanar da zaben gaskiya .Kuma kasar Kenya kamar Nijeriya tana da mutumci da tasiri a yankin gabashin Afrika dama Afrika gabaki daya.Shugaba Mwai Kibaki dan shekara 76 a duniya bai yi halalci ba, bai kuma sa bukatun kasar kan bukatun sa ba.Da anyi zaben son zuciya kamar yadda yayi a yanzu da bai hau kan kujerar mulkin kasar ba .A yau ya jefa kasar sa cikin kashe-kashe da fadan kabilanci wanda zai raba kan jama'ar kasar da maida ita baya a fannonin cigaba.Boren da jama'ar kasar keyi ya nuna a fili bashi suka zaba ba kuma sun gaji da salon mulkin sa.

Matsalar magudin zabe nada illar gaske ga kuma sa duk shugaban da yazo ta hanyar rashin samun kwarin gwiwa ya bugi kirji ya aiwatar da ayyukan cigaba saboda rashin halarci da jin linzamin wadanda suka daura shi. A karshe sukan koma wajen Amerika da Turawan Yamma dan samin yarda a madadin aiwatar da bukatu da manufofin su. Gubar magudin zabe na kara yaduwa in kasashen da ya kamata su zama abin koyi ga wasu kasashe a Afrika suma suka tsinci kansu a matsalar magudin zabe kamar Nijeriya . Ga kasar Kenya tabi sahu,wacce abar koyi ce ga kasashen gabashin Afrika.

Kasar Kenya ta tsinci kanta a wani hali na ban takaici da kunya saboda son zuciya na wasu shugabannin ta , inda a yanzu sun bude gabar kiyayya a tsakanin kabilun kasar su, inda talakawa da basu ji ba basu gani ba ake ta karkashe wa da kwasar ganima da kone dukiyoyin su. Shugabannnin kasashen Afrika nada bukatar canza takun su game da yanda ya kamata a gudanar da zabe domin cigaba da bunkasar tsarin dimokaradiya a nahiyar mu.


Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Sunday, 30 December 2007

Benazir Bhutto: Mace Mai Kamar Maza !

Ranar 27 ga watan Disambar 2007 zai kasance bakar rana a tarihin kasar Pakistan da gun masu gwagwarmayar kafuwa da dorewar tsarin dimokaradiya a duniya,saboda kisan gillar da akayi wa Malama Benazir Bhutto , tsohuwar Firaministan kasar Pakistan kuma mace ta farko data fara rike babban mukamin siyasa a kasar Musulmi a wannan zamanin.

An haife ta ranar 21 ga watan Yuni na shekarar 1953 a birnin Karachi na kasar Pakistan. Ta kuma yi karatu a manyan jami'oi wato Havard a Amurka da Oxford a Birtaniya.Mahaifinta Marigayi Zulfikar Ali ya gamu da ajalin sa ta hanyar rataya a hannun sojoji masu mulkin kasar a lokacin karkashin jagorancin Janar Zia Ul Haqq. Itama bata tsira ba daga mulkin danniya na sojojin kasar inda aka kama ta tare da tsare ta na tsawon shekaru kafin a sake ta, ta kuma bar kasar a shekarar 1984. A shekarar 1986 ta sake komawa Pakistan inda ta sami gagarumin tarba daga jama'ar kasar. Ta tsaya takara a karkashin jam'iyyar Pakistan People's Party(PPP) inda ta sami nasara ta kuma kasance Firaminista tana da shekaru talatin da biyar a duniya.

A lokacin mulkin ta, ta samar da wutar lantarki a kauyukan kasar da kuma gina makarantu a ko'ina cikin kasar.Manyan manufofin gwamnatin ta sune kokarin kawo karshen yunwa da samar da gidaje masu saukin kudi ga iyalai da gina asibitoci da lamurran da suka shafi kula da lafiya a birane da kauyukan kasar. Tayi matukar kokari wajen ganin cewa kasar ta , ta sami cigaban zamani kamar sauran kasashen yankin.

Zargin cin hanci da sama da fadi da dukiyar al'umma yasa shugaban kasa na lokacin Shugaba Leghari ya rushe gwamnatin ta, aka kuma damke mijin ta aka daure shi, ganin yanda abubuwa suka kasance , sai ta sake barin Pakistan ,inda ta shafe kusan shekaru goma ita da ya'yanta suna gudun hijiran sa kai a birnin Landan. Kuma duk da cewa bata kasar amma bata yi kasa a gwiwa ba wajen ganin cewa an dawo da mulkin dimokaradiya a kasar Pakistan ba.

Duk da barazanar da take fuskanta daga masu adawa da ita, ta koma kasar Pakistan a watan Octoban da ta gabata, ta kuma tsira daga harin kunan bakin waken da aka kai mata wanda yayi sanadiyar rasuwar mutane fiye da dari .Amma harin da aka sake kai mata a garin Rawalpindi yayi sanadiyar mutuwar ta da wasu mutum ashirin.

Shaka babu rasuwar Benazir Bhutto zai samar da babban gibi a siyasar Pakistan , musamman zaben da ake shirin gabatarwa ranar 8 ga watan Janairu . Jam'iyyar ta na PPP nada farin jini da tasiri da karfin gaske a kasar wanda saboda hakkar ta da tasirin da zata iya yi nema Janar Pervez Musharraf yayi wa tsohon firaminista Nawaz Sharif afuwa shima ya dawo kasar domin rage karfin Benazir Bhutto da yarjejeniyar da ta kulla da Janar Musharraf ya rushe na tayi masa firaminista.

Kasar Pakistan ta sake samun kanta a tsaka mai wuya sakamakon kisan Benazir Bhutto . Shi kansa Musharraf yana cikin halin bayan sa Kura gaban sa Zaki saboda magoya bayan Benazir Bhutto na ganin cewa ya kasa bata cikakken tsaro duk da barazanar da take fuskan ta daga masu adawa da ita. Ta bangaren gwamnati sun daura zargin kisan nata akan kungiyoyin al-Kaida da Taliban.Wata kungiyar masu tsattsauran ra'ayin addini sun nisan ta kan su daga daukar alhakin kisan nata. Ta bangaren magoya bayan Benazir Bhutto sun nuna shakkun su kan cewa jagoran sojin sa kai Baitullah Mehsud nada hannu a kisan nata duk da ikirarin da yayi na cewa zasu tura dan kunan bakin wake ya tarbe ta duk lokacin data dawo Pakistan.

Malama Benazir Bhutto ta shafe kusan shekaru shida na rayuwar ta a tsare a gidan kurkuku ko a hannun jami'an tsaro.Yan'uwan ta biyu wato Murtaza da Shahnawaz suma a baya kashe su aka yi. A shekarar 1977 lokacin da aka tsare mahaifin ta bayan juyin mulkin da Janar Zia ya jagoran ta , ya tuhume shi da laifin kisan kai, inda bayan shekaru biyu aka rataye shi. An daure Benazir Bhutto kafin a kashe mahaifin ta, inda ekaru biyar a gidan kurkuku, kuma yanda ta fada a wani yanayi mai wahalar gaske.

Ta zama Firaministan kasar Pakistan a shekarun 1988 zuwa 1990 da 1993 zuwa 1996. Tay matukar kokarin ta wajen ganin cewa an yafe wa juna abubuwan da suka faru a shekarun baya a kasar da kokarin ganin cewqa an rage banbancin da ake nunawa tsakanin maza da mata.

Kafin dawowar ta Pakistan ,wasu yan kasar na zargin ta da ganawa da sojoji masu mulkin kasar , inda sukayi tataunawar sirri domin a bata damar taka wata rawa ta musamman a siyasar kasar.Wannan yasa wasu yan kasar na zargin ta da cin amanar tsarin bunkasar dimokaradiya a asar.Inda wasu kuma na ganin cewa tattaunawar nada amfanu ga kafuwar dimokaradiya a kasar. Su kuma kasashen Yamma na ganin cewa goyon baya da karbuwa da take dashi a kasar ,tunda ta kasan ce tanada sassaucin ra'ayi na iya baiwa Janar Musharraf halarci a da'awar sa na "yaki da ta'addanci".

A jawaban ta marigayiya Benazir Bhutto bata boye fahimtar ta kan masu tsattsauran ra'ayin addinin Musulunci ba, kan yanda suke gudanar da al'amurran su a kasar, inda tayi alkawarin in aka zabe ta zata samo hanyar da yafi dacewa wajen magan ce matsalar tsattsauran ra'ayin addini sabanin yanda Janar Musharraf ke tinkaran lamarin.Ta kuma yi alkawarin cewa zata cika alkawarorin da Musharraf ya kasa cikawa kan batun makarantun madarasah inda zata aiwatar da sauye-sauyean makarantun, zata kuma baiwa hukumar IAEA damar ganawa da Abdulkadir Khan kan fasahar nukiliyar Pakistan.

Mutuwar Benazir Bhutto yasa ta cimma manufofinta da ta kasa cimma lokacin da take raye.Yanda ta gamu da ajalinta ya sanya duk an mance da kurakuran da ake ganin ta tafka lokacin data jagoranci kasar a baya. A ko'ina cikin duniya an kadu da mutuwar ta inda shugabanin kasashen duniya sukayi jawaban kwarai a kanta.Kuma ga dukan alamu mutuwar nata zai bude sabon babi a gwagwarmayar kafuwar dimokaradiya a kasar Pakistan da makomar Janar Musharraf da kuma yadda kasar zata tinkari matsalar masu tsattsauran ra'ayin addini. Kasar Pakisatan na dab da fadawa cikin mumunan yanayin siyasa koma yakin basasa sakamakon kashe Benazir Bhutto. Matsalar da kasar ta sami kanta ya zarce matsalar cikin gida ko yanki. Pakistan kasa ce da masu tsananin kishin addinin Musulunci keda tasiri a siyasan ce, kuma kasar nada fasahar makamin nukiliya wanda wadannan dalilai biyu barazana ce ga kasar Amerika da Turai.

Tarihi zai ruwaito Benazir Bhutto a matsayin wata mace data tsaya kai da fata kan akidu da manufofin da tayi imani dasu ba tare da jin tsoro ba, tasa kasar ta agaba duk da barazanar da take fuskanta har ta bar duniya tana kan gwagwarmayar inganta rayuwar al'umman kasar ta.

Haza Wassalam,

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Monday, 17 December 2007

LABARIN ZOMO DA MANGWARO

Wata rana ne Zomo na tsalle-tsallen sa yana tunanin zuci,daya karaso karkashin wata bishiyar Mangoro yana daga kansa sama sai ya hango wani Mangoro jajawur, ga girma kuma gashi ya nuna sosai.Ganin haka ya fara tunanin yaya zai yi ya sami Mangwaron dan shi ba zai iya hawa bishiyar ba. Yana tunanin yanda zai yi sai ga Kurciya ta sauka a kan bishiyar Mangwaron.Tana hango Zomo tayi masa sallama "barka dai "shima Zomo ya maida gaisuwar "kaima barka dai" Sannan ya kara da cewa "taimaka mani Kurciya ki tsinkar mani wancan Mangoron".

Kurciya a take ta tashi ta kusanci Mangwaron dan ta tsinka .Domin yawun ta ya tsinke da ganin mangoron kuma tayi tunanin ta cinye shi ita kadai. Amma da ta tsinki Mangoron sai ta kasa rikewa da bakin ta ,sakamakon haka sai Mangoron ya fado kasa.

Zomo na ganin haka cikin murna yac wa Kurciya"nagode" ya sun kuya ya dauki Mangwaro sai ya gan Mangwaron nata gungurawa daga gare shi , kai kamar Mangoron ne da kan sa ke gungurawa.Mamaki ya kama Zomo yana cewa" anya Mangoro da kansa zai yi ta gungurawa haka! Yana dubawa da kyau sai ya lura da cewa Mangoron ya fado ne a bayan Bushiya ya kuma makale a jikin kayoyin dake jikin ta. Shi yasa in ta motsa sai Mangoron ma ya motsa. Bushiya na ganin mangwaro a bayan sa ,ya yanke shawarar cewa Mangoron nasa ne kuma gashi da son Mangwaro. A take sai ya yanke shawarar ya arcen da Mangoron. Zomo na ganin haka ya kwada masa kira yana "tsaya! tsaya! dawo! Ina zaka da Mangoro na? Bushiya na jin haka sai ya samu waje ya tsaya, yace ma Zomo "Mangoron nan a baya na ya fado saboda haka Mangwaron nan nawa ne" . Kurciya na kallon su sai tace "kai, ku daina gardama a zancen gaskiya Mangoro dai nawa ne dan ni na tsinko shi daga kan bishiya". Haka dai suka rinka gardama da rants-rantse kan cewa ko wannen su na da'awar cewa Mangoro nasa ne.

Suna cikin wannan yamutsin sai ga Kare yazo wuce wa .Sai ya tsaya yana kallon hayaniya da tada jijiyoyin wuya da suke yi. Sai yace masu"wai kan me kuke wannan daga murya? Sai duk suka taho wajen sa , sai dayan su ya kada baki yace"Kare ka kasance mai hikima da kwarewa sakamakon zaman ka da mutane, saboda haka muna son kayi mana shari'a bisa adalci kan wanda yafi cancanta ya tafi da wannan Mangoro". Sai ko wannen su ya bashi labarin dalilin sa na cewa Mangoro nasa ne. Kare yayi tunani ,sai ya tambaya "wa ya fara ganin Mangoron ? Sai Zomo ya kada baki yace "ni ne! ni ne ! Sai kare ya sake tambaya "wa ya tsinko Mangoro? Sai Kurciya tayi tsalle ta ce "ni ce! ni ce na tsinko! Sai kare ya sake tambaya " wa ya dauki Mangoro bayan an tsinko? Sai Bushiya ya ce "ni ne! ni ne domin a baya na ya fado! Sai Kare ya yanke masu hukunci kan cewa "matsalar da kuke fuskanta shine ko wannan ku nada iko akan Mangoro, amma Mangoro guda daya ne , saboda haka na yanke hukuncin cewa za'a raba maku Mangoro ku daidai gida uku".

Mamaki da murna ya kama dabbobin gaba daya kan hukuncin da Kare ya yanke masu. A take Bushiya ya dauko Mangoro daga bayan sa ,ya raba gida hudu. Ya fara mika wa Zomo "ga rabon ka saboda fara ganin Mangoro". Sai ya mika wa kurciya yana cewa "ga naki rabon dan tsinko mangoron da kika yi". Sai ya baiwa kansa wani bangaren yace "saboda ya fado a baya na". Sannan ya baiwa Kare wani bangaren yace "ga naka " Kare yayi mamakin gaske cike da farin ciki sai ya ce "me yasa nima kuka bani wani bangaren a matsayin rabo na?" Sai Bushiya ya ce "saboda ka bamu shawaran da muka ji dadi ". Ta wannan hanyar dukkan su suka sami rabon shan Mangoro mai dadi cikin jin dadi da annashuwa.

Darasin da wannan labarin ke koyar wa ita ce raba dai dai aiki ne mai kyau domin yana kawo farin ciki da warware matsaloli da dama.

Haza wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Wednesday, 10 October 2007

ARE TRADITIONAL AND RELIGIOUS LEADERS IN SUPPORT OF THE MASSES?

By Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Among community leaders in Nigeria, the traditional and religious leaders do receive special respect from the people as they are regarded as fathers of the society. They are regarded as burning candles that show the way on how the society should live based on their forms of belief. Also it is their duty on commanding the community on performance of good deeds and forbidding them to commit what is unlawful.

Masses had a very special regards and respect for traditional and religious leaders as they believed that they would never support and encourage any issue that will harm their ways of life. But unfortunately, recently some of them have reversed and changed their attitude by becoming errand boys of those in power and moneybags. It is an open secret today that many of them have joined the club and convoy of the ruling class or always in total support of any government in power.

Clerics as religious leaders all over the world are known to be on the side of justice ,truth, equity and accountability, and they also preach to their followers to be on the side of truth and justice. They are steadfast as they are never afraid to say the truth and side with justice no matter how bitter it is. Also they never collaborate with oppressors, tyrants, looters and ungodly leaders. Religious history books are full of narrations of how God fearing clerics fought against injustice, tyranny and suppression. Some of them had even led their countries in the fight against uprooting tyrants, oppressors and stooges from power. They are actively involved in the fight against all forms of injustice and discrimination against their people and even in the forefront in the struggle for democratic governance.

Even during our present times we saw or heard of religious leaders that have led their people to defeat tyranny and oppression, and those that were persecuted and jailed or were forced to exile or even killed for saying and siding with the truth and justice by some few individuals who have control of the government machinery.

Today, before our own eyes, some Clerics have changed the meanings and interpretations of their Holy Books to suit the intrest of political leaders so that they could smile back to their banks. What is happening today is that if you force your way corruptly to power through massively rigged election, they will say God gave you the power! If you loot from the treasury they will say God has enriched you !! If you implement policies against the wishes of the people, they will say God said you should be followed!!! Also you will find these Clerics on their ways to government houses federal, state and local or in the homes of those that all knows how they amass their wealth.

Am not saying that it is an offence for traditional and religious leaders to relate with the political and ruling class, but what is happening always is that they don't inform the ruling class the real condition of the masses and the country. Masses are really suffering due to lack of infrastructures. But the traditional and religious leaders never speak up and always pretend as if everything is moving smoothly. Whenever they speak it is on the masses to always live peacefully and abide by the laws without speaking out to the ruling class to rule with justice and equity.

It can't be denied that traditional and religious leaders have special prestige in Nigeria. Is it that the prestige they have is not enough that they have to be errands of the political class? And are there any worldly materials they lacked that led them to be boot licker of the political class? Are they aware that masses can now dictate their personal intrest when they propagate it as religious injuctions? Are they of the opinion that being errand and cohorts for those in power is the only avenue to protect their seats and gain influence? And when will they seek respect for themselves as true leaders of the society and people stop calling them agents of whoever is in power?

Traditional and religious leaders are those leaders that the masses tend to have good opinion about as they provide guidance and protect their rights when the need arises. Is it not a betrayal that these leaders tend to be more concerned about their own personal interests? Don’t they think that the masses can have a very bad opinion about them?

The history of many countries of this world is full of roles played by Kings and the Clergy. Why is it that today in some parts of the world they tend to play little or no role in such countries today? The answer is clear as these leaders par take in the exploitation and tyranny against their own people and when change arrived those countries they were not spared. And that is the reason why in some countries there are no traces of traditional rulers and the religious leaders lose their prestige and power of commanding the good and forbidding evil.

Where are those traditional rulers that have supported election riggers into power? The history of our country is replete with how those helped to hold onto power illegitimately repay their benefactors? Also religious leaders that sided with the authority against the wish and aspirations of their people tend to lose respect and dignity as they are viewed as agents and cohorts of those in power.

Respect and prestige will be more for traditional and religious leaders if they side with the masses. And they should have the principle of advising the ruling class truthfully, and informing them of how life of the common man can be improved and stoppage of all government policies that are anti-people. And if they happen to visit government houses from federal to local government it should be for the intrest of the masses not to seek for contracts, royalties and political appointments for themselves and families. Also they should be bold enough to say the truth to the ruling class as they can say it to the masses. They should be in the forefront in any struggle to resist government policies that are unpopular such as increase in petroleum products but not the NLC!

God fearing and purposeful leadership is loved by people. Any leader that loots either before or now should not be seen associating with traditional and religious leaders as such association increases the continuation of corruption as future leaders can always think that if they loot and share the loot through building places or worship and obtaining traditional titles they will be respected and escape justice. Traditional and religious leaders should reciprocate to the masses the same way they hold them in esteem; anything short of this could lead to anarchy as it will be unfortunate if they call people to order and no one listens to them, then who will provide guidance to the society?

Saturday, 6 October 2007

Badakalar kwangila :Ya wajaba Etteh Tayi Murabus!

Mace ta farko da ta fara rike mukami mafi girma a Nigeria wato Uwargida Patricia Olubunmi Etteh na shugabantar majalisar wakilai na cikin tsaka mai wuya ko kuma ace tana cikin halin dana sani saboda halin da ta tsinci kanta na badakalar zargin aringizon kwangilar kwaskwarimar gidanta da mataimakinta Hon. Babangida Nguroje da motocin alfarma guda goma sha biyu kan tsabar kudi naira miliyan dari shida da ashirin da takwas!

Kamar yadda kwamitin Idoko ya bada rahoton sa ,sun sami shugabar majalisar da laifi dunu-dumu kan zargin da ake yi mata inda kwamitin ya gano cewa ba'a ma bi tsarin daya kamata ba wajen bada kwangilolin,domin da farko ba'a tallata kwangilar ba a jaridu ,na biyu kanfanonin dake kwangilar basu da rajista da hukuma da wasu laifufukan da kwamitin ya bankado.Amma ita Uwargida Etteh ta dage kan cewa bata da laifi saboda haka ba zata amsa kiraye-kirayen da ake tayi mata ba na tayi murabus ko ta fuskanci tsigewa.

Mafi yawan 'yan Nigeria nada ra'ayin cewa a wannan halin da talakawa ke cikin bakin talauci da fatara ace an sami shugabar majalisar wakilai ta kashe zunzurutun kudi na miliyoyin nairori har sama da dari shida saboda kwaskwarimar gidaje da sayen motocin alfarma bai dace ba.Sannan wasu na ganin cewa bata ma chancanci rike mukamin ba saboda rashin gogewa da ilimi mai zurfi,saboda sana'ar data goge a kanta itace na gyran gashi!Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ne ya dankara wa 'yan Nijeriya ita saboda dalilan dashi kansa yafi kowa sani.

Tun lokacin da wasu 'yan majalisar wakilai karkashin lemar "Integrity Group" bisa jagorancin Hon.Faruk Lawan da John Halims Agoda Da Mercy Almona Isei suka shiga gwagwarmayar ganin Etteh ta rabu da kujerar ta magoya bayan ta ke zargin su da cewa suna wannan kaiwa da komowa ne saboda basu sami biyan bukatun su ba na shugabantar kwamitocin majalisar masu maiko. Shi dai Hon.Faruk Lawan shine jagoran wadanda suka tsaya har Etteh ta kujerar shugabancin majalisar wakilai an kuma wayi gari a yau shine jagoran masu son ganin bayan ta !

Bankado badakalar aringizon kwangilolin gyran gigan su Uwargida Etteh ke da wuya harkokin majalisar wakilai ya tsaya chak.Rabon majalisar ta zauna domin tattauna da tsara dokoki an kwana biyu saboda Etteh na fargaban majalisa ta zauna dan bata san yadda za'a kwashe ba. Lallai Uwargida Etteh ta tafka abun kunya da Allah-wadai ,ta kuma zubar da mutunci da kimar majalisar tarayya a idanun 'yan Nijeriya saboda haka ya zama wajibi ,ya zamo tilas tayi murabus! In kuma taki to lallai ya wajaba ga 'yan majalisar wakilai su tasa keyar ta , ta hanyar tsigewa sannan hukumomin yaki da cin hanci da almundahana suyi aikin su a kanta.

In har da gaske gwamnatin Alhaji Umaru Musa 'Yar'adua keyi na da'awar yaki da cin hanci da rub da ciki da dukiyar al'umma to su shawarce ta tayi murabus domin tana rike da mukami mai muhimmancin gaske na tsara wa kasa dokoki.Sannan zai zama wata dama ga gwamnatin na 'Yar'adua su rabu da yan amshin shatar Obasanjo da suke nema suyi wa gwamnatin sa kene-kane.

Ya kuma kamata Uwargida Etteh ta amsa kiraye-kirayen da shugabanin siyasa da addini da al'umma keyi mata na tayi murabus .Wannan kiraye -kiraye da ake yi mata ya nuna cewa a fili bata da goyon bayan 'yan Nijeriya,Sannan inda wani mutunci ko martaba da suke anin ta dashi ,to ya zube.Ita kuma a kokarinta na ganin cewa bata sauka daga kujerar ta na shugabantar majalisar waklai ba ta dauki wasu matakai da zasu kara jefa ta cikin tsaka mai wuya.Domin da farko tayi amfani da kabilanci ,inda ta kaiwa Alhaji Lamidi Adedibu ziyara shi kuma yayi maganganun neman tada zaune tsaye inda ya dangata matsalar ta da makomar kabilar 'Yarbawa.Haka kuma taso tayi amfani da addini inda ta bada umarnin masallacin dake gidanta mazauni sannan ta gina majami'a.

Ya kamata ta san da cewa ba wai 'yan Nijeriya sun tsane ta bane dan kawai tana mace ko Bayarabiya ba a'a suna ganin cewa bukatun kanta da jin dadin ta kawai shine a gaban ta.Saboda labarai dake fitowa game da ita suna nunawa ne zuwa ga almubazaranci.Tayi bikin kece raini a ranar zagayowar ranar haihuwar ta a kasar Amurka,ga kuma neman da tayi a saya mata injin tausa na miliyoyin nairori! Ga kuma wannan badakalar na kwaskwariman gida, gaidan da kwanannan Alhaji Aminu Bello Masari ya fita a cikin sa bayan zama na shekaru hudu da yayi.

Uwargida Etteh ta baiwa 'yan Nijeriya musamman mata da kabilar ta na 'Yarbawa kunya.Domin kungiyoyin mata da suka yi ta tsalle-tsalle na murnan ganin cewa hakar su ta fara cimma ruwa na ganin cewa ana damawa dasu a kololuwar siyasar Nijeriya ta basu kunya domin ta aikata abinda mazan da suka jagoranci majalisar basu aikata ba.Ta bangaren kabilar ta na 'Yarbawa ta sake dama masu lissafi domin ya sake bayyana a gare su cewa halin bera da handama da babakere bai takaita ga wasu kabila ko yankin kasar ba a'a matsala ce dake tattare da rashin adalci da rikon amana da kishin kasa.

In 'yan majalisar wakilai suka yi nasarar kawar da Etteh ko kuma taga haza tayi murabus a kashin kanta,to ya kamata suyi kyakyawan nazari bisa mahangar adalci kan wanda zaifi dacewa ya ko ta jagoranci majalisar.Cikin abubuwan da zasu duba shine na zaben wanda ake ganin cewa baya fuskantar barazanar soke zaben sa saboda tafka magudin zabe a gaban kuliya manta sabo.Da kuma duba mutumin da suke ganin cewa ba zai zama karen farauta ko dan amshin shata ga "Aso Rock"ba.Irin shugaban da suka zabar ma kan su shine madubin da al'umma zasu yi ta kollon su dashi.Misali irin shugabancin da Aljaji Ghali Umar Na'abba yayi wa majalisar wakilai a zango na farko ya bata daraja da kwarjini a idon 'yan Nijeriya da kasashen waje.Haka ma shugabancin da Alhaji Aminu Bello Masari yayi wa majalisar shi ya bata ruhin da ta sami chajin murkushe tazarce.

Lokaci yayi da Uwargida Patricia Etteh zata amsa kiran yan Nijeriya tayi murabus.Kasantuwar ta da cigaba da jagorantar majalisar wakilai ba a bin amincewa bane ga 'yan Nijeriya saboda ta bayyana tana da laifi a badakalar kwangilolin kwaskwarimar gidanta dana mataimakin ta kamar yadda rahoton kwamitin Idoko ya bayyana.Mutunci madara ne in .....

Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

Sunday, 30 September 2007

TUNAWA DA RANAR KUDUS: RANAR JADDADA GOYON BAYA GA PALASTINAWA

A watan Yuli na shekarar 1979 marigayi Imamu Ruhullah al-Khomeini(r.a)ya bada fatawa ga al'ummar Musulmin duniya da masoya 'yanci da adalci na cewa kowace ranar Jumma'a ta karshen watan Ramalana ta kasance ranar Kudus. Kuma wannan fatawar ita ta canza al-kiblar gwagwarmayar Kudus da Palastinawa daga gwagwarmayar yan kasanci da Larabawa zuwa wani al'amari da ya hau kan al'ummar Musulmin duniya.

Menene Ranar Kudus? Kudus ta kasance Palastinu ga al'ummar Musulmi,ga su kuma Yahudawa ta kasance kasar Isra'ila. A kasar Kudus Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas yake inda ya kasance al-Kibla ta farko ga Musulmi ,kuma Masallaci na uku mafi daraja bayan Ka'aba mai girma da Masallacin Manzo Muhammad(saw)dake garin Madinatun Munauwara.

Ranar Kudus ta kasance rana ta hadin kai a tsakanin Musulmin duniya domin tunkarar matsalar Kudus da ta kasance abunda ya shafi dukkan Musulmi,kuma ranar Kudus ta kasance ranar da Musulmin duniya zasu isar da sako da murya guda domin al'ummar duniya ta sani ko a sake tunatar da ita irin zaluncin da danniya da kama karya da cin mutumcin da Yahudawan kasar mamaya ta Isra'ila kewa al'ummar Palastinawa dama Musulmi musamman kasashen Musulmin dake makotaka da Isra'ila.Ranar Kudus ta kuma kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tattauna tare da nemo mafita game da halin da al'ummar Palastinu suka sami kan su da tono da bankado irin makirce-makircen da kasar mamaya ta Isra'ila kewa Palastinawa da al'ummar Musulmi a ko'ina cikin duniya.

Shekarun bayan yakin duniya na biyu zasu kasance a bin tunawa da jimami ba wai ga al'ummar Palastinu da Musulmi kadai ba ,a'a harma da masoya 'yanci da adalci da walwala a ko'ina cikin duniya saboda mamayar zalunci da mulkin mallaka na babakere da Isra'ila tayi wa Palastinu.Sannan labari ne sananne ta yadda kasar Isra'ila ta jera shekaru tana karkashe Palastinawa mata da yara da tsofaffi,tare da rusa masu gidaje da gonaki da makarantu da asibitoci da wuraren sana'a da tilastawa dubun dubatan Palastinawa hijira zuwa wasu kasashe .Duk da irin zaluncin keta da ta'asar da Isra'ila keta aikatawa har yanzu ,kasashen dake da'awar 'yanci da kare hakkin dan-adam da dimokaradiya ke tallafawa Isra'ila da bata cikakken kwarin gwiwa kan abinda take aikatawa na assha ga al'ummar Palastinu musamman kasar Amerika.

Ranar Kudus rana ce ta masoya yanci da adalci da zaman lafiya da daidaituwa da mutumta hakkin dan-adam a ko'ina cikin duniya wadanda suke nuna goyon bayan su ga Palastinawa da ake zalunta da kuma kokarin isar da sakon halin kakani-kayin da Palastinawa ke ciki ga wadanda basu sani ba ko kuma suka jahilci halin da Palastinawa e ciki a hannun kasar Isra'ila .Kuma ranar Kudus ta kasance ranar da al'ummar Musulmi zasu tunatar da kawunan su cewa Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas baya karkashin kulawar su da ikon su.Kazalika Ranar Kudus ta kasance ranar da kusan shekaru ashirin al'ummar Musulmi dake da wayewa ta siyasar duniya dama wadanda ba Musulmi ba da suka tsani zalunci da danniya ke isar da sakonni ta hanyoyin da yafi yi masu sauki na isar da sakon su na Allah -wadai ga kasar mamayar Isra'ila da nema wa Palastinawa da ake zaluntagoyon baya domin al'ummar duniya su tallafa masu.

Ranar Kudus ta kasance rana ta musamman saboda ta kasance ranar da ake sake jaddada goyon baya ga al'ummar Palastinawa wanda Musulmin duniya keyi harma da masoya 'yanci a ko'ina cikin duniya.Ranar Kudus rana ce ta sake samun natsuwa a zukatan Musulmin duniya da Palastinawa kan sanin cewa dole wata rana Kudus ta komo hannun Musulmi da Palastinawa.

Mu rika tunawa da Ranar Kudus ta hanyoyin da zamu iya koda kuwa yaya yake domin mu nuna wa al'ummar Palastinawa da ake zalunta cewa muna tare da su, su kuma kasar mamaya ta Isra'ila su san da cewa bama goyon bayan ta'assar da suke aikatawa sannan muna Allah-wadai da zaluncin da suke aikatawa.Sannan mu sake jaddada muhimmancin Masallacin al-Aksa ko Baitul-Mukaddas ga Musulmin duniya.

Haza Wassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com