Wednesday 19 March 2008

Vincent Ogulafor ; Ko zai sake wa tuwo suna?

Yemira Vincent Ogulafor shine sabon shugaban jam'iyyar PDP na kasa.Ya zamo shugaban jam'iyyar ne sabannin harsashen masana harkokin siyasa dake ganin za'a fafata ne tsakanin tsohon gwamnan jihar Ebonyi Sam Egwu mai samun goton bayan tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Sanata Anyim Pius Anyim tsohon shugaban majalisar dattijai dake samun goyon bayan masu adawa da Cif Olusegun Obasanjo, amma sai Ogulafor ya kasance shugaba saboda samun goyon bayan gwamnonin jam'iyyar da yayi.

Kasan tuwan jam'iyyar PDP, jam'iyyar dake mulkin kasa yan Nijeriya zasu cigaba dasa mata ido kan yadda take tafiyar da al'amurran ta.Yanda take fassara tsarin dimokaradiyya na zama abin koyi ga sauran jam'iyyun adawa.Saboda yanda ake ganin jam'iyyar PDP keyi na zama abun koyi ga sauran jam'iyyu,misali yanda ake gudanar da zaben kananan hukumomi a jihohin da take mulki na samun kwaikwayon jihohin da jam'iyyun adawa ke mulki.Kazalika yanda suke tafiyar da harkokin su na zaben fidda gwani da zaben shugabanni na zama abin koyi ga jam'iyyun adawa.

Yan Nijeriya zasu cigaba dasa ido kan yadda Ogulafor zai tafiyar da jam'iyyar musamman siyasar cikin gidan jam'iyyar inda ake dankara wa yan jam'iyya yan takara da bashi suke soba ko kuma sukama zaba ba a lokutan zabubbukan fidda gwani . Sannan za'a sa ido kan yanda zai dawo da daraja da martabar jam'iyyar a idanun yan Nijeriya. Ga talakawan, sukan danganta duk wani cuta ko fin karfi ko kwace ko babakere ko handama ga jam'iyyar PDP.

Ogulafor a baya ya kasance sakataren jam'iyyar na kasa har na tsawon shekaru shida. Sun yi hannun riga ne da tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo kan zanen tazarce a karo na uku. Ya kasance cikin yan jam'iyyar da suka ki amincewa da wannan burin na Obasanjo.

Amma abin lura game da yanda Ogulafor zai tafiyar da jam'iyyar shine na in zai iya adalci kan batutuwan da zasu taso nan gaba da suka shafi gwamnonin jam'iyyar ganin cewa su suka daura shi bisa kujeran shugabancin jam'iyyar. Shin zai yi adalci a zabubbukan fidda gwani daya shafi gwamnonin PDP dama na Shugaban kasa? Tuni har ya fito fili ya fadawa yan Nijeriya cewa zai mika wuya kashi dari har da daya ga shugaban kasa Umaru Musa Yar'adua. Irin mika wuyan da Dakta Ahmadu Ali tsohon shugaban jam'iyyar yayi ga tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya janyo rudanin da jam'iyyar ta sami kanta da kuma zubar da kimar kasar nan a kasashen duniya game da lamuran zabe. Mika wuyan da Ahmadu Ali yayi yasa Obasanjo yaso ya canza kundin tsarin mulkin kasar nan dan samun zango na uku da kuma yan majalisar dattijai sukayi watsi da zancen ya kiya su "yan iska". Sannan mika wuyan shi ya janyo maye gurbin yan takara da wasu daban da rudanin daya janyo kotuna na nada wadanda basu tsaya zabe ba a matsayin gwamnoni da yan majalisa saboda su suka lashe zaben fidda gwani amma akayi masu fin karfi aka daura wasu daban.

Kalubalen dake gaban Ogulafor sun hada da shin zai iya dawo da martaban jam'iyyar PDP ? Shin zai iya jagorantar yan jam'iyyar domin aiwatar da manufofin jam'iyyar dake zancen inganta rayuwan yan Nijeriya ?Sannan zai iya karkafafa karfin jam'iyya da ikon ya kan masu mukamai na gwamnati?Kuma shin zai iya jagorantar jam'iyyar ba tare da yarda wasu suna tsoma baki ba ko su mayar dashi dan amshin shatar su ba?

Akwai ayyuka masu yawan gaske a gaban Ogulafor inda gaske yake. Misali aiwatar da shawarwarin da kwamitin sulhu da tsohon mataimakin shigaban kasa Alex Ekwueme kewa shugabanci da aka ajiye rahoton a gefe, dan in anyi amfani da rahoton kwamitin watakila wasu yan jam'iyyar ada zasu komo jam'iyyar kamar yanda Alhaji Abubakar Rimi da Alhaji Ghali Umar Na'abba suka dawo jam'iyyar . Da kuma daidaita tsarin shugabancin jam'iyyar a jihohi inda wasu magoya bayan Obasanjo suka mamayeshugabancin jam'iyyar . Sannan ko zai iya taimakawa wajen amsa kiran yan jam'iyyar na dawowa da tsohon kudin tsari mulkin jam'iyyar dan raba Obasanjo da shugabantar kwamitin amintattu na jam'iyyar.

Da sannu yan Nijeriya zasu fahimci salon jagoranci irin na Ogulafor domin ta haka kawai za'a banbanta shi dasu Barnabas Gemade da Audu Ogbeh da Ahmadu Ali da a lokutan su akayi watsi da manufofin jam'iyyar aka rika gasa wa talakawa aya a hannun su, su kuma suka tsuke bakunan su har tasu ta hada su da Obasanjo.Haka kuma yan Nijeriya zasu sa masa ido su gani ko zai yi jagorancin sa bisa gaskiya da adalci da rikon amana da mutumta yan jam'iyya wanda ta haka zai iya sa yan Nijeriya su canza tunanin su bisa jam'iyyar PDP kan yadda Obasanjo ya tilasta masu suke kallon ta.

Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

No comments:

Post a Comment