Saturday 8 March 2008

Talakawan Nijeriya na rayuwa cikin matsi.

In banda karfin hali irin na yan Nijeriya,musamman ma talakawa ba,da sun fara begen gwamnatin baya saboda yanda a kullum rayuwar yau da kullum sai kara wahala saboda yanda kayan abinci keta kara farashi kamar kullun waina.

Talakawan Nijeriya a yau na rayuwa cikin matsi domin kullum yaje kasuwa sai ya tarar da hauhawan farashin kayayyakin masarufi da kusan kashi arba'in zuwa hamsin.Shi kuma abunda yake samu in ma yana da abinyi babu wani kari da yake samu dake tafiya dai-dai da hauhawan farashin kayayyaki.

Ta bangaren tsaro kuma har yau a tsare hanya ayi wa jama'a kwace har da raba su da rayukan su sai cigaba yake.Hanyoyin da a shekarun baya ba'a san yan fashi da makami da tare su ba, suma yan fashi na tarewa a yanzu suna yin fashi har da kisa,,kai kace ko babu jami'an tsaro a kasar.

A yau a kasar nan in talaka ya kamu da rashin lafiya to lallai kashin sa ya bushe.Tsakanin talaka da asibiti sai kallo domin ba zai iya biyan kudaden da suke cazan mara lafiya ba. Sai dai ya sha maganin gargajiya in ya dace ya warke. In kuma rashin lafiyar ya shafi tiyata ko magunguna masu tsada to sai dai in yana da hanya a nemi taimako gun jama'a ta kafofin watsa labarai ko ya kwanta a gida ya saurari mutuwa.Saboda yanda gwamnati keta zame hannuwan ta game da harkar lafiya a yau sana'ar saida maganin bature dana gargajiya da asibitoci masu zaman kansu ya zama harka mai ribar gaske.

Ilimi zamani dama na addini mai inganci yafi karfin talaka.In har kana son ya'yan ka su sami ilimi mai inganci to lallai sai suna zuwa makarantu masu zaman kansu . Sanin cewa ilimi tsani ne ga samun rayuwa mai dadi da daukaka a rayuwar duniya,kamar yadda a yau ya'yan talakawa suka sami dama mai yawa a rayuwar su har da shugabantar al'ummomin su , sai gashi a yau karatu ya gagari dan talaka. Yan boko sunyi amfani da damar da suka samu wajen hana ya'yan talakawa samun ilimi dama raba kan al'umma saboda da ya'yan talakawa da ya'yan masu shuni ba zasu taba haduwa ba ,saboda makarantun su daga firamare zuwa jami'a daban-daban ne.

Rashin aikin yi na cikin abubuwan dake cima talakawa tuwo a kwarya. Sana'oi da kasuwancin da talakawa ke tabawa sun cushe saboda yawan masu yin ta. Misali sana'ar Achaba ko Aski ko saida katin waya ko tireda ko leburanci da sauran su anyi masu yawa har ba'a iya samun na masarufi.Rashin wutar lantarki yasa kamfanoni da masana'antu masu yawa sun rufe wanda zasu iya baiwa dubbban jama'a aikin yi. Masu aikin gwamnati ko manya kamfanoni na cikin fargaba a kullum na rasa aiyukan su,saboda kila a cigaba da raba mutane da aikin su kamar a lokacin gwamnatin baya.

A lokutan zabe tuni talakan Nijeriya kuri'ar sa ta rasa muhimmanci saboda wanda zai zaba daban ,wanda za'a dankara masa daban.Da zabe ya gabato sai shugabanin kasa dana gargajiya dana addini su fito suna umartan talakawa su fito zabe, talakawa kan amsa kiran su ,su fito mazan su da matan su su yi zabe. Amma abin takaici shine sai a tafka magudi sannan a fito a fada masu cewa cin zabe ta haramtacciyar hanya daga Allah ne ! Saboda halin ya bunburutun siyasa na rubda ciki da kuri'oin talakawa lallai talakawa zasu sake tunani a zabubbukan gaba nasu daina zabe gaba daya domin babu bukatar fitowa su bata lokacin su.

Duk da halin matsin rayuwa da talaka ya sami kansa a yau na tsadan kayayyakin masarufi babu wani malamin addini ko basaraken gargajiya ko kungiyoyin bangaranci ko shugabanin siyasa daga shugaban kasa zuwa kansila daya nemi a kawo wa talaka dauki, in ma sunyi magana to dogon turanci ne dama yin shiru shi yafi. Yanda yan amshin shatar gwamnati ke fitowa dan kalubalantar masu neman hakkin su , basa iya fitowa su fadawa gwamnati cewa yunwa na neman kassara talakawa domin tsadar abinci ya wuce hankali.

Rainin hankali da wulakancin da ake yiwa talakawan Nijeriya zai cigaba in har suka kasa banbance adalci da kabilanci da bangaranci. Cikin dabarun da masu mulkin kasar nan ke amfani da ita wajen cigaba da danne su shine na canza taku da zarar talakawa zasu gane, wato tsarin mulkin karba -karba,alhalin su masu mulki dodo daya suke yiwa tsafi. In talakawa zasu cigaba da yarda da zancen mulki yankin su ko kuma wanda suke addini daya dashi ba tare da lura da cancantar sa da hanyar daya ya zama mai mulki ba ,to za'a dade ana shan wahala.

Lokaci kuma yayi da talakawan Nijeriya zasu daina yarda ana mai dasu mara yanci a kasar su ta haihuwa. Kad su gaza ga neman hakkokin su da tsarin mulkin kasa ya basu bisa dokar kasa. Kada su yarda da farfagandar da ake yadawa na cewa Nijeriya ba zata taba gyaruwa ba, mu fara da gyara tunanin mu na cewa Nijeriya zata gyaru kuma tama fi wasu kasashen duniya dake da'awar cigaba. Kowa ya sani matsalar Nijeriya na rashin samun kyakyawan shugabanci ne, duk ranar da tayi dace da shugaba mai kishin al'ummar sa , mai magana daya , wanda ya zama shugaba bisa halartacciyar hanya, jarumi ba matsoraci ba , to lallai kasar mu zata cigaba.

Kuma talakawa su gane dabarun masu mulkin kasar nan na wofitar da tunanin mutane na yanda nan gaba in lokacin zabe yazo zasu ci karen su babu babbaka. A gobe za'a sake zabe talakawa su fito zabe su kuma yi iyakar iyawan su wajen ganin anyi zabe na gaskiya kamar yadda ta kasance a wasu jihohi a zabubbukan baya..In suka yarda suka mika wuya ta hanyar kin fitowa zabubbuka a nan gaba to zasu cigaba da zama karkashin mulkin fin karfi da sunan dimokaradiyya.

Hakki ne daya rataya akan talakawan Nijeriya su taka wa yan cuwa-cuwan siyasa burki dan cigaban kasar mu. In har talakawa zasu yarda a saye su kan naira dari biyu da sabulan wanki , to basu yiwa kansu da kasar su adalci ba.Ko'ina cikin duniya ana ta cigaba musamman kasashe masu albarkatun man fetur da dangogin sa inda abincin talaka shine shinkafa da madara da kaji, amma mu a kasar mu duk da arzikin mu garin kwaki da tuwon hatsi na gagaran talaka sau uku a rana. Yan siyasar mu har gobe cigaban gwamnatocin su shine gina kwalbatoci da rijiyoyi da rumfuna!

Wajibi ne ga talakawan Nijeriya su tashi tsaye dan a basu hakkokin su da tsarin mulkin kasa ya basu. Kin yin haka zai sa su kasance cikin rayuwan kaskanci da rayuwa maras tabbas ga ya'yan su da jikokin su. Bamu da wata kasa data wuce Nijeriya saboda haka dole mu tsaya mu ceche ta dan kawunan mu da bayan mu.

Hazawassalam

Shehu Mustapha Chaji
shehuchaji@yahoo.com

No comments:

Post a Comment